Ana Neman Daukar Karin Matakin Kawar Da Shingayen Dake Hana ‘Ya’ya Mata Zuwa Makaranta A Zamfara
Published: 11th, August 2025 GMT
Mahalarta taron masu ruwa da tsaki na yini daya don tabbatar da sakamakon bincike kan al’amuran zamantakewa da suka shafi ilimin ‘ya’ya mata a jihar Zamfara, sun bukaci iyaye, shugabannin al’umma, da gwamnati a dukkan matakai da su magance matsalolin da ke hana yara mata zuwa kammala karatun sakandare.
Kungiyar AGILE da ke Jihar Zamfara tare da hadin gwiwar Media and Publicity Consult ta shirya taron masu ruwa da tsaki na rana daya domin tabbatar da sakamakon binciken da aka yi kan ka’idojin zamantakewa da ke kawo cikas ga ’yan mata matasa da ke hana shiga makarantun gaba da sakandare a jihar Zamfara.
Da yake jawabi a wajen taron, Farfesa Abubakar Aliyu Liman na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, ya jaddada bukatar masu ruwa da tsaki su samar da yanayi mai kyau da zai karfafa gwiwar ‘ya’ya mata su ci gaba da karatu.
Farfesa Liman, wanda kuma shi ne babban mai ba da shawara kan aikin bincike na AGILE a Zamfara, ya bayyana cewa auren dole da rashin goyon bayan iyaye a matsayin wasu manyan matsalolin da suka shafi ilimin ‘ya’ya mata a jihar.
Wakilan Ma’aikatun Mata da Ilimi na Jihar Zamfara sun yaba da tasirin aikin AGILE a Zamfara tare da yin kira da a ci gaba da inganta ayyukan da suka hada da samar da ingantattun hanyoyin ruwa, tsaftar muhalli a makarantu.
Mataimakin kodinetan hukumar AGILE a jihar Zamfara, Dakta Salisu Dalhatu, ya bayyana cewa an kammala makarantu 317 daga cikin 440 da aka ware domin gyarawa a karkashin hukumar ta AGILE, yayin da sama da ‘yan mata 8,000 ke cin gajiyar shirin bayar da tallafin kudi.
Manajan Daraktan yada labarai da tuntuba (MPC), Malam Nasiru Usman Biyabiki, ya ce taron tabbatar da shi an yi shi ne da nufin tace sakamakon binciken don samun ingantacciyar hanyar shiga tsakani.
A cewarsa, gangamin wayar da kan jama’a ya taimaka wajen ganin jihar Zamfara ta kasance cikin jerin jahohi biyar da suka fi aiwatar da ayyukan AGILE a fadin kasar nan.
Taron wanda MPC ta kira, ya kuma yi nazari kan sakamakon da Daraktar ICT ta kungiyar, Hibban Buhari ta gabatar, wanda ya bayyana talauci, al’adu, auren dole, da rashin ingantaccen tsarin karatu a matsayin manyan abubuwan da ke kawo tarnaki ga ‘ya’ya mata da kuma rike su.
Binciken ya ba da shawarar yin amfani da harsunan Hausa, Fulfulde, da Larabci wajen kamfen na wayar da kan jama’a, inda rediyon ya zama cibiyar farko saboda yawan isar da sako.
AMINU DALHATU.Gusau
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: a jihar Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Jarumar Kannywood Rahama Sadau ta yi aure
Fitacciyar jarumar Kannywood, Rahama Sadau, ta yi aure da masoyinta, Ibrahim Garba.
An ɗaura auren a ranar Asabar a Masallacin da ke Unguwan Rimi, a Jihar Kaduna, bayan Ibrahim ya biya sadaki Naira 300,000.
Za a biya ma’aikata 445 garatutin sama da biliyan ɗaya a Kebbi Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfaraRahama, ta sanar da ɗaurin auren a shafinta na Facebook, inda ta gode wa Allah tare da neman addu’a daga masoyanta.
Ta bayyana farin ciki da godiyarta, tare da fatan wannan sabon babi na rayuwarta zai kasance mai albarka.
Auren mata na zuwa ne watanni biyu bayan rasuwar mahaifinta, Ibrahim Sadau.
’Yan uwanta sun yaɗa hotuna da bidiyon bikin a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama suka yi mamakin yadda aka yi bikin ba tare da sanin jama’a ba.
Rahama, wacce furodusa ce a Kannywood, an naɗa ta memba a Kwamitin Fasaha na shirin Investment in Digital and Creative Enterprise (iDICE).
An ba ta muƙamin ne a 2024 ƙarƙashin ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima.