Aminiya:
2025-09-24@09:57:04 GMT

Mahaifin Ɗan Bello ya rasu

Published: 8th, August 2025 GMT

Fitaccen matashin nan mai barkwanci, Bello Habib Galadanci, wanda aka fi sani da Ɗan Bello, ya yi rashin mahaifinsa a yammacin wannan Alhamis din.

Matashin lauyan nan ɗan gwagwarmaya, Abba Hikima, ne ya bayyana hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano NAHCON ta ƙayyade N8.

5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026

“Innalillahi wa inna IlaiHi rajiun. Allah Ya yi wa Mahaifin Dokta Bello Galadanchi (Dan Bello) rasuwa yanzun nan. Allah Ya gafarta masa. Ameen,” a cewar saƙon da Abba Hikima ya wallafa.

Kawo yanzu dai ba a bayyana dalilin rasuwar mahaifin Ɗan Bellon ba, amma wasu kafofin watsa labarai sun ruwaito cewa marigayi ya rasu bayan fama da jinya.

Ɗan Bello ya kasance dan gwagwarmaya marar tsoro da ake ganin na daga cikin matasa da za su iya kawo sauyi a ƙasar nan.

Matashin ya sha ƙalubalantar gwamnatocin jihohi har ma da tarayya kan sakaci da walwalar al’ummar da suke jagoranta musamman a bangaren ilimi da kuma harkokin lafiya domin zaburar da su kan abin da ya kamata.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Hukumar Tsaron Farin Kaya DSS ta riƙe matashin na dan lokaci taƙaitacce yayin saukarsa a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano bayan shigowarsa ƙasar daga China.

Ɗan Bello dai ya yi ƙaurin suna wajen yin bidiyon barkwanci kan matsalolin shugabanci da cin hanci a Nijeriya.

A kwanan baya wasu saƙonni da ya wallafa kan matsalar fanshon ’yan sanda da ta matsalar albashin malaman jami’a sun ɗauki hankali matuƙa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Bello

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa ta amince da ’yancin ƙasar Falasɗinu a hukumance

Faransa ta bi sahun Birtaniya, Australia da Canada da sauran ƙasashen duniya sama da 140 da suka amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai ’yanci.

Shugaban Faransa, Emmanuel Macron ne ya tabbatar da amincewar gwamnatinsa na kafa ƙasar Falasdinu a hukumance.

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙara haɓaka — NBS NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa

Macron ya bayar da tabbacin ne a yayin da yake jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York.

Mista Macron ya ce lokaci ya yi da ya kamata a kawo ƙarshen yaƙin Gaza tare da sakin sauran Isra’ilawa 48 da Hamas ke garkuwa da su.

Ya ce lokaci kaɗan ne ya rage wa duniya ta iya wanzar da zaman lafiya, don haka ya ce bai kamata a jira ba.

Mista Macron ya yi Allah-wadai da harin na ranar 7 ga watan Oktoba da Hamas ta kai wa Isra’ila.

Shugaban na Faransa ya ce yana son ganin an samar da zaman lafiya a yankin ta hanyar samar da ƙasashe biyu masu cin gashin kai da ke zama makwabtan juna.

“Babu wata hujja na ci gaba da yaƙin Gaza”, in ji Macron, yana mai ƙarawa da cewa “ya kamata a kawo ƙarshen komai.”

A yau ne dai tawagar jami’an diflomasiyyan Falasɗinu ta gudanar da bikin ɗaga tutar ƙasar a birnin Landan, kwana guda bayan da Birtaniya ta amince da Falasɗinu a matsayin kasa mai cin gashin kanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh ya rasu yana da shekara 82
  • ’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a Kebbi
  • Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025
  • Faransa ta amince da ’yancin ƙasar Falasɗinu a hukumance
  • An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya
  • Sarkin Ruman Katsina ya rasu
  • Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike
  • Hatsarin mota ya yi ajalin mutum 4, 16 sun jikkata a Yobe
  • Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu