Aminiya:
2025-11-28@11:34:36 GMT

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan

Published: 10th, August 2025 GMT

Dubban mutane ne suka fito kan tituna a birnin Tel Aviv na Isra’ila ranar Asabar, domin yin kira da a kawo ƙarshen yaƙin Gaza, kwana guda bayan da gwamnatin Isra’ila ta lashi takobin faɗaɗa rikicin tare da ƙwace birnin Gaza.

Masu zanga-zangar da ke riƙe da hotunan waɗanda har yanzu ake garkuwa da su a yankin Falasdinawa sun yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da sakin su ’yan uwansu.

Al-Hilal ta ɗauki Nunez daga Liverpool ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki

’Yan jaridar AFP a wajen gangamin sun ƙiyasta adadin waɗanda suka halarci taron a matsayin dubbai, yayin da wata ƙungiya da ke wakiltar iyalan wadanda aka yi garkuwa da su ta ce mutane kusan 100,000 ne suka yi dafifi.

Hukumomin ƙasar ba su bada wasu alƙaluma mutane da suka shiga zanga-zangar ba, amma sun hakikance lalai ya, zarta duk wasu gangamin da aka yi a baya na adawa da yakin.

Masu zanga-zangar sun ƙarkare da aike wa Firaminista Benjamin Netanyahu saƙo da kakkausar murya.

Shahar Mor Zahiro, ɗaya daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da ɗan uwansa, ya shaida wa AFP cewar: “Idan ka mamaye sauran sassan Gaza kuma aka kashe sauran ’yan uwanmu da ake garkuwa da su, za mu bi ka har cikin harabar dandalin Square, ko a lokacin yakin neman zaɓe ko a kowane lokaci ko waje.”

A ranar Juma’ar da ta gabata, majalisar ministocin tsaron Netanyahu ta amince da gagarumin farmaki na kwace birnin Gaza, lamarin da ya janyo cece-kuce da tofin Allah tsine daga cikin gida da ƙasashen duniya.

Wasu ƙasashen ketare, ciki har da wasu kawayen Isra’ila, sun yi ta matsa kaimi don ganin an tsagaita wuta domin tabbatar da dawowar wadanda aka yi garkuwa da su da kuma taimakawa wajen rage matsalar jin kai a yankin.

Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasɗinu a Istanbul

Dubban masu zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu sun taru a Dandalin Beyazit na Istanbul a ranar Asabar bayan sallar Magariba, domin nuna adawarsu ga kisan kiyashi da ƙaƙaba yunwa da Isra’ila ke yi a Gaza.

Gangamin, wanda ya haɗa da ƙungiyoyin ba da gwamnati da kuma jama’a da dama, ya ci gaba da tafiya zuwa Masallaci mai tarihi na Ayasofya.

Mahalarta sun yi ƙoƙarin jan hankalin duniya game da matsalar jin kai da ke faruwa a Gaza, tare da nuna goyon baya gare su, yayin da tashin hankali da ƙarancin abinci da magunguna ke ƙara ta’azzara.

Masu shirya zanga-zangar sun yi kira ga al’ummar duniya da su ɗauki matakan gaggawa don kawo ƙarshen wahalhalun.

Isra’ila Na Fuskantar Matsin Lamba Daga Duniya

Isra’ila na fuskantar ƙarin fushin duniya saboda kisan kiyashi da take yi a Gaza, inda ta kashe fiye da mutane 61,000 tun watan Oktoba 2023.

Haren-haren da soja ke kaiwa sun lalata yankin sosai kuma sun haifar da mutuwa ta hanyar yunwa da ƙunci.

A watan Nuwamba da ya gabata, Kotun Hukunta Laifukan Yaƙi ta Duniya ta bayar da sammacin kama Firayiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohon Ministan Tsaronsa Yoav Gallant saboda laifukan yaƙi da laifukan cin zarafin ɗan adam a Gaza.

Haka kuma, Isra’ila tana fuskantar shari’ar kisan kiyashi a Kotun Duniya saboda yaƙin da take yi a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila garkuwa da su zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza

Rahotanni sun bayyana cewa kididdigar da ma’aikatar harkokin wajen yankin falasdinu ta fitar ya nuna cewa sojojin Isra’ila sun kashe akalla yan mata 33000 a ci gaba da yakin kare dangi da take yi kan alummar Gaza.

Ma’aikatar fa fitar da wannan sanarwar ce a wajen taron ranar kawo karshen hare-hare kan mata ta duniya . kuma tayi kaca-kaca da gwamnatin sahayuniya game da irin muggan laifukan yaki da ta tafka, inda ta rika amfani da makamai na zamani kan alummar falasdinu

Kididdigar ta nuna cewa sama da mata 12500 da kuma yara 20,000 ne Isra’ila ta kashe a harin da ta kai tun daga watan oktoban shekara ta 2023.

Har ila yau ma’aikatar ta bayyana cewa lallai a kwai bukatar a dauki matakin gaggawa na matsin lamba domin kawo karshen ci gaba da mamaye yankunan falasdinawa da HKI ke yi, kuma tayi aiki da kudurin kafa kasashe guda biyu da zai bada garanti wajen kafa kasar falasdinu..

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa November 26, 2025 Sojojin Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar  Guinea Bissau November 26, 2025 Larijani Iran Tana Maraba Da Tattaunawa Ta Gaskiya Amma Ba Tsararren Sakamako Ba November 26, 2025   November 26, 2025 Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza November 26, 2025 Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe November 26, 2025 Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta November 26, 2025 Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki November 26, 2025 Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana
  • Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Zanga-Zangar Lumana
  • DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza