Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Published: 9th, August 2025 GMT
“Kuma za a yi hakan ne saboda a matsayinmu na al’umma, muna ci gaba da ƙoƙarin canza abubuwan da ‘yan siyasa ba sa son canzawa,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa ba yau aka fara aikin gyaran kundin tsarin mulkin ƙasar kan batun cin gashin kan ƙananan hukumomi ba.
Ejah ya ƙara da cewa ana sa ran kashi biyu cikin uku na ‘yan majalisar wakilai za su kaɗa ƙuri’ar amincewa ko kuma ƙin amincewa da gyaran.
Ya ƙara da cewa gwamnatin Bola Tinubu ta bayar da umarnin ne kawai, biyo bayan hukuncin da kotun ƙoli ta yanke, cewa a biya kason kuɗaɗen da majalisun za su samu kai tsaye a asusunsu.
A cewarsa, wannan ba gyara ba ne, domin kuwa sai an zagaya jihohi 36 yadda al’umma za su mara masa baya kafin ya zama doka.
“Abin da muka yi shi ne yunƙurin zartarwa na ganin ƙananan hukumomi sun samu kuɗaɗensu kai tsaye amma hakan ba zai yi tasiri ba saboda tanade-tanaden hukuncin kotun ƙoli bai wuce tsarin mulki ba,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tattalin arzikin Najeriya ya ƙara haɓaka — NBS
Hukumar Ƙididdigar a Najeriya, NBS ta ce arzikin cikin gida da ƙasar ke samu ya ƙaru da kashi 4.23 cikin 100 a rubu’i na biyu na shekarar 2025 da muke ciki.
Sabbin alƙaluman da hukumar ta fitar sun nuna cewa an samu ƙarin kashi 3.48, idan aka kwatanta da daidai wannan lokacin a 2024, lamarin da hukumar ta ce alamu ne na bunƙasar tattalin arzikin ƙasar.
An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AINBS ta ce fannin aikin gona ne kan gaba wajen samar da ƙaruwar arzikin ƙasar, wanda ya ƙaru zuwa kashi 2.82 saɓanin kashi 2.60 a 2024.
Sauran fannonin da hukumar ta ce an samu ci gaba sun hada da fannin masana’antu da, da man fetur da kuma fannin ma’adinai.
NBS ta ce a rubu’i na biyu na shekarar 2025, arzikin cikin gida da Najeriya ta samu ya kai naira tiriliyan 100.73, ƙari kan naira tiriliyan 84.48 da aka samu a 2024 daidai wannan lokacin, abin da ke nuna ƙarin kashi 19.23 cikin 100.
A watan jiya na Agusta ne Majalisar Ƙoli ta tattalin arziki a Najeriya, ta sanar da amincewa da sabon tsarin ci gaban tattalin arziki zango na biyu na tsawon shekaru 5 wato 2026-2030, bayan ƙarewar zangon farko wato daga 2021 zuwa 2025.
Sabon tsarin da majalisar ta ƙaddamar wadda ke ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shetima ci gaban tattalin arziki zai yi la’akari da sauye-sauyen da aka samu kamar cire tallafin man fetur, sabbin dokokin haraji da makamatansu.
Ƙarƙashin sabon tsari ne kuma gwamnatin ke son cimma ƙarfin tattalin arziƙi na Dala tiriliyan ɗaya nan da shekarar 2030, abinda ya dace da manufofin ƙasar har zuwa shekarar 2050.