Tankokin mai sun yi bindiga a Zariya
Published: 11th, August 2025 GMT
Wasu manyan motocin dakon sun yi bindiga a yankin Ɗan Magaji da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna.
Ana fargabar mutuwar mutane da dama sakamakon gobarar tankokin man bayan sun yi hastari a safiyar Litinin.
Shaidu sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:30 na safe a kusa da Makarantar Rochas Foundation, kan titin Kaduna–Kano bypass daga Kwangila zuwa Dan Magaji.
Hatsarin ya haɗa da manyan motoci biyu masu ɗauke da man fetur da kuma motoci biyu ƙirar Golf ɗauke da fasinjoji.
A sakamakon haka, tankokin biyu suka yi bindiga, wanda ya tayar da wutar gobara mai ƙarfi tare da hayaƙi mai kauri ya lulluɓe hanyar.
Jami’an ceto da tsaro sun rufe hanyar, tare da gargaɗin direbobi da su guji bi ta wurin yayin da ake ci gaba da aikin ceto da dawo da gawarwaki.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ana Neman Daukar Karin Matakin Kawar Da Shingayen Dake Hana ‘Ya’ya Mata Zuwa Makaranta A Zamfara
Mahalarta taron masu ruwa da tsaki na yini daya don tabbatar da sakamakon bincike kan al’amuran zamantakewa da suka shafi ilimin ‘ya’ya mata a jihar Zamfara, sun bukaci iyaye, shugabannin al’umma, da gwamnati a dukkan matakai da su magance matsalolin da ke hana yara mata zuwa kammala karatun sakandare.
Kungiyar AGILE da ke Jihar Zamfara tare da hadin gwiwar Media and Publicity Consult ta shirya taron masu ruwa da tsaki na rana daya domin tabbatar da sakamakon binciken da aka yi kan ka’idojin zamantakewa da ke kawo cikas ga ’yan mata matasa da ke hana shiga makarantun gaba da sakandare a jihar Zamfara.
Da yake jawabi a wajen taron, Farfesa Abubakar Aliyu Liman na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, ya jaddada bukatar masu ruwa da tsaki su samar da yanayi mai kyau da zai karfafa gwiwar ‘ya’ya mata su ci gaba da karatu.
Farfesa Liman, wanda kuma shi ne babban mai ba da shawara kan aikin bincike na AGILE a Zamfara, ya bayyana cewa auren dole da rashin goyon bayan iyaye a matsayin wasu manyan matsalolin da suka shafi ilimin ‘ya’ya mata a jihar.
Wakilan Ma’aikatun Mata da Ilimi na Jihar Zamfara sun yaba da tasirin aikin AGILE a Zamfara tare da yin kira da a ci gaba da inganta ayyukan da suka hada da samar da ingantattun hanyoyin ruwa, tsaftar muhalli a makarantu.
Mataimakin kodinetan hukumar AGILE a jihar Zamfara, Dakta Salisu Dalhatu, ya bayyana cewa an kammala makarantu 317 daga cikin 440 da aka ware domin gyarawa a karkashin hukumar ta AGILE, yayin da sama da ‘yan mata 8,000 ke cin gajiyar shirin bayar da tallafin kudi.
Manajan Daraktan yada labarai da tuntuba (MPC), Malam Nasiru Usman Biyabiki, ya ce taron tabbatar da shi an yi shi ne da nufin tace sakamakon binciken don samun ingantacciyar hanyar shiga tsakani.
A cewarsa, gangamin wayar da kan jama’a ya taimaka wajen ganin jihar Zamfara ta kasance cikin jerin jahohi biyar da suka fi aiwatar da ayyukan AGILE a fadin kasar nan.
Taron wanda MPC ta kira, ya kuma yi nazari kan sakamakon da Daraktar ICT ta kungiyar, Hibban Buhari ta gabatar, wanda ya bayyana talauci, al’adu, auren dole, da rashin ingantaccen tsarin karatu a matsayin manyan abubuwan da ke kawo tarnaki ga ‘ya’ya mata da kuma rike su.
Binciken ya ba da shawarar yin amfani da harsunan Hausa, Fulfulde, da Larabci wajen kamfen na wayar da kan jama’a, inda rediyon ya zama cibiyar farko saboda yawan isar da sako.
AMINU DALHATU.Gusau