An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa
Published: 11th, August 2025 GMT
Hukumar tsaro ta sibil difens (NSCDC) ta sanar da cafke wani mutum, Salisu Muhammad, mai shekaru 45, bisa zargin kashe jami’inta, Bashir Adamu Jibrin, a kasuwar Shuwarin da ke Karamar Hukumar Kiyawa a Jihar Jigawa.
A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Muhammed Badarudeen ya fitar a Dutse, babban birnin jihar, lamarin ya faru ne a ranar kasuwa lokacin da marigayin yake gudanar da aikinsa.
Rahotanni sun nuna cewa, ana zargin Salisu ya buga wa jami’in dutse a kai, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa.
Hukumar ta ce ta kama wanda ake zargin ne a gidansa da ke Shuwarin a ranar 7 ga watan Agusta, 2025.
Sai dai bayanai sun ce Salisu wanda bai cimma nasara ba yayi ƙoƙarin tserewa a yayin da ake jigilar sa zuwa hedikwatar NSCDC da ke Dutse a cikin motar jami’an tsaron.
Sanarwar ta ƙara da cewa, Salisu ya samu raunuka ne yayin da yake ƙoƙarin tserewa, kuma daga bisani aka kai shi babban asibitin Dutse, inda aka tabbatar da rasuwarsa sakamakon raunikan da ya samu.
Sai dai ’yan uwansa sun buƙaci cikakken bayani dangane da raunikan da ya samu har da dalilin rasuwarsa a asibitin Sambo Limited wanda aka garzaya da shi bayan ya yi yunƙrin tserewa daga mota da ke tafe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta cafke wasu mutane shida da ake zargin ‘yan fashi da makami da masu garkuwa da mutane ne a karamar hukumar Doma da ke jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Ramhan Nansel ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a lafiya, ya ce jami’an sun kuma kama wani makiyayi dauke da makamai a karamar hukumar Keana ta jihar.
Sanarwar ta ce, jami’an sashin Doma da ke aiki da sahihan bayanan sirri daga wani dan kasa mai kishin kasa, karkashin jagorancin jami’in ‘yan sandan shiyya, sun kai samame a wata maboyar ‘yan ta’adda da ke Yelwa Ediya inda aka kama wadanda ake zargin.
Ya ce a yayin da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun amsa laifin yin garkuwa da wani kansila mai ci inda suka sace wayoyin hannunsa guda biyu.
Sun kuma amince da cewa sun tare hanyar Doma zuwa Yelwa ne inda suka kai hari kan wani Ibrahim Haruna Yelwa Ediya tare da kwace babur dinsa kirar Bajaj wanda kudinsa ya kai ₦970,000 yayin da ake sayar da babur din da suka sace.
SP Ramhan Nansel ya bayyana cewa, a yayin aikin jami’an sun kwato kudi ₦100,000 – kudaden da aka siyar da babur din da aka binne a daji, tare da babur Bajaj daya.
A wani labarin makamancin haka, jami’an sashin Keana sun amsa kiran da suka yi na cewa makiyayan da ke kiwo a filayen gonaki a Gidan Zaki Hassan da ke karamar hukumar Kuduku a karamar hukumar Keana, yayin da makiyayan suka yi ta harbe-harbe kafin su gudu.
‘Yan sandan da ke aiki da jama’ar gari sun kama wani makiyayi mai shekaru 20, sannan sun kwato bindiga samfurin AK-47 guda daya dauke da harsashi guda shida.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Shattima Jauro Mohammed, ya bayar da umarnin mika duk wadanda ake tuhuma zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar domin gudanar da bincike mai zurfi tare da gurfanar da su gaban kuliya.
CP Mohammed ya jaddada kudirin rundunar na tabbatar da zaman lafiya ga kowa da kowa, yana mai gargadin cewa ba za a samu mafaka ga masu aikata laifuka ba.
Ya bukaci mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda kuma su ci gaba da bayar da bayanai masu inganci a kan lokaci don taimakawa ayyukan ‘yan sanda.
Rel/Aliyu Muraki/Lafia.