Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
Published: 8th, August 2025 GMT
Idan aka dubi wannan, bai kamata a riƙa ɓata karatu ana cewa Masallaci ne za a ziyarta amma ba Annabi (SAW) ba. Ya kamata a gyara karatu, a gyara wannan fahimtar. Saboda irin wannan fahimtar ce ta haifar da a zamanin nan an samu rashin girmama Manzon Allah (SAW) har aka dasa bom kusa da shi. Ko ɗaga murya Allah ya hana a yi a gaban Annabi (SAW), to ina ga tada bom?
A huɗubar sallar Idil Fiɗir da Limamin Makka ya yi a Harami, ya ce Yahudawa ne suka tada bom ɗin, amma sai ga shi da Saudiyya ta nuna wanda ya yi abin, da sunanshi da kamanninsa har da dogon gemu, ɗan ƙasar ne mai iƙirarin bin Salafiyya Sunnah.
Malamai Malikawa sun yi hukuncin cewa zuwa ziyara a Madina wajibi ne ga wanda yake da hali. Ma’ana idan mutum ya yi Aikin Hajji, wajibi ne ya ziyarci Manzon Allah (SAW) idan yana da halin zuwa.
Masu cewa idan mutum ya yi Hajji shikenan ba sai ya tafi ziyarar ba, suna nuna alama ce ta ƙin Manzon Allah (SAW).
Hadisai masu yawa sun yi bayani a kan falalar ziyarar Manzon Allah (SAW).
Yana daga ciki, Abdullahi bin Umar (RA) ya ruwaito cewa, Manzon Allah (SAW) ya ce, “Duk wanda ya yi Hajji, sai ya ziyarci ƙabarina bayan mutuwata, ya zama kamar wanda ya ziyarce ni ne lokacin da nake da rai.” Ma’ana duk ɗaya suke.
Asƙalani, mai sharhin Bukhari ya ce zuwa Madina iri biyu ne, ana zuwa a lokacin da Manzon Allah (SAW) yake raye a kan ƙasa domin a karɓi shiriya, bayan wafatinsa kuma a je a ziyarci ƙabarinsa (SAW).
Dukkanin malamai na Allah Ahlus Sunnah tun daga kan Sahabbai a kan wannan fahimtar suke.
Haka nan, Hadisi ya tabbata daga Abdullahi bin Umar (RA) cewa, Manzon Allah (SAW) ya ce, “Duk wanda ya ziyarci ƙabarina, cetona ya cancanta a gare shi”. Abu Haraira (RA) ya ruwaito Hadisi daga Manzon Allah (SAW) ya ce, “Babu wani mutum da zai yi sallama a gare ni, face Allah ya dawo mun da raina har na amsa sallamar.”
Idan mutum zai je ziyarar, walau Alhaji ko wanda ba Alhaji ba, zai yi niyyar cewa zai je ya ziyarci Manzon Allah (SAW), sannan ya yi sallah a Masallacinsa, ya ziyarci sauran Sahabbai da wuraren Musulunci. Amma dai Annabi (SAW) ne a kan gaba.
Ana so idan mai ziyara ya tasam ma Madinar Annabi (SAW), ya yawaita salati ga Manzon Allah (SAW) domin ya ƙara samun haske da soyayyarsa (SAW).
Haka nan, ana so mutum ya yi wanka, ya sa turare, ya sa tufafinsa mafi kyau, kuma ya jaddada tubansa, sannan ya halarto da girman Annabi (SAW) a cikin zuciyarsa, da girman Sahabbansa, da ganin girman garin baki ɗaya (a matsayin wurin da Annabi (SAW) da Iyalansa da Sahabbansa suka rayu, da faruwar abubuwan tarihi na Musulunci. Lallai idan mutum ya yi haka, zai ji wani ƙarin imani har ya sa shi kuka.
Idan mai ziyara ya zo shiga Masallacin Annabi (SAW), ana so ya shiga da ƙafar dama ya ce “A’uzubillahil azim wa bi wajhihil karim wa sulɗanihil ƙadim minas shaiɗanir rajim, bismillah, allahumma salli ala Muhammadin wa alihi wa sallim, allahummagfirli zunubi waftahali abwaba rahmatika.”
Idan da hali ya yi ƙoƙari ya shiga Raula (wurin da Annabi ya ce Dausayin Aljanna ne) ya yi sallah nafila raka’a biyu a matsayin gaisuwar Masallaci. Idan kuma Raula ta cika, sai a yi sallar a duk wurin da aka samu a Masallacin.
Ana so idan mai ziyara ya tasam ma Madinar Annabi (SAW), ya yawaita salati ga Manzon Allah (SAW) domin ya ƙara samun haske da soyayyarsa (SAW).
Haka nan, ana so mutum ya yi wanka, ya sa turare, ya sa tufafinsa mafi kyau, kuma ya jaddada tubansa, sannan ya halarto da girman Annabi (SAW) a cikin zuciyarsa, da girman Sahabbansa, da ganin girman garin baki ɗaya (a matsayin wurin da Annabi (SAW) da Iyalansa da Sahabbansa suka rayu, da faruwar abubuwan tarihi na Musulunci. Lallai idan mutum ya yi haka, zai ji wani ƙarin imani har ya sa shi kuka.
Idan mai ziyara ya zo shiga Masallacin Annabi (SAW), ana so ya shiga da ƙafar dama ya ce “A’uzubillahil azim wa bi wajhihil karim wa sulɗanihil ƙadim minas shaiɗanir rajim, bismillah, allahumma salli ala Muhammadin wa alihi wa sallim, allahummagfirli zunubi waftahali abwaba rahmatika.”
Idan da hali ya yi ƙoƙari ya shiga Raula (wurin da Annabi ya ce Dausayin Aljanna ne) ya yi sallah nafila raka’a biyu a matsayin gaisuwar Masallaci. Idan kuma Raula ta cika, sai a yi sallar a duk wurin da aka samu a Masallacin.
Daga nan, idan lokacin ya kasance lokacin sallar farilla ne sai ya tsaya a kammala sallar, idan kuma ba lokacinta ne ba, yana idar da nafilar sai ya nufi ziyarar Annabi (SAW).
Idan ya zo wurin ƙabarin mai girma, sai ya baiwa alƙibla baya; ya fuskanci bangon ƙabarin kusa da inda hukuma ta amince a tsaya. Ya halarto da girman Annabi (SAW) tare da tunanin cewa ga fuskar Annabi (SAW) tana kallonsa. Sai ya yi sallama cikin ladabi na sarari da ɓoye, sannan ya yi salati ga Manzon Allah (SAW). Ma’ana ya ce”Assalamu alaika ya Rasulullah, assalamu alaika ya Nabiyyallah, assalamu alaika ya Khaira khalƙillah, assallamu alaika ya Habiballah, assalamu alaika ya Sayyidal Murasalin, assalamu alaika ya rasula Rabbul alamin, assalamu alaika ya ƙa’ida gurril muhajjalin. Ash’hadu an la’ilaha illallah wa ash’hadu annaka abduhu wa rasuluhu wa aminuhu wa khiratuhu Wa ash’hadu annaka ƙad ballagtar risalata wa addaital amanata wa nasahtal ummata wa jahada fillahi haƙƙa jihadihi.”
Sai mutum ya karanta ayar nan ta neman gafarar Allah a wurinsa (SAW) ta cikin Suratun Nisa’i. Idan ya samu hali sai ya ɗan ja baya kaɗan ya yi salati guda 70 ga Annabi (SAW).
Daga nan ya matsa daidai kamu ɗaya a dama, ya yi sallama ga Sayyidina Abubakar (RA), kuma ya ƙara matsawa irin haka duk dai a dama, ya yi sallama ga Sayyidina Umar (RA). Daga nan sai ya fice ya kammala ziyara.
Dangane da juya wa aklbla baya a kalli fuskar Annabi (SAW) lokacin da mutum zai yi addu’a, an ruwaito cewa Abu Ja’afarul Mansur Al-Abbas (Sarkin Musulmi) ya tambayi Imam Malik (RA) da ya zo ziyara cewa, “Shin Annabi (SAW) zan fuskanta in yi addu’a ko alƙibla?” Sai ya amsa ma sa da cewa “Don me za ka kawar da fuskarka ga Manzon Allah (SAW) alhali shi ne tsaninka kuma tsanin Babanka Adamu (AS) zuwa ga Allah?”. Saboda haka mai ziyara ya fuskanci Annabi (SAW) ya yi addu’a.
Amma da yake hukumar can ta yanzu ba su yarda a kalli Annabi (SAW) a yi addu’a ba, to sai mutum ya kalli Alƙibla sai ya halarto da shi (SAW) a zuciya. Kuma koda ma alƙiblar aka kalla dole sai an bi ta wurin Annabi saboda mutum zai yi salatinsa (SAW) a cikin addu’ar.
Akwai wasu da suke nuna wa Alhazai cewa ba koyaushe ne suka shiga Masallaci sai sun ziyarci Annabi (SAW) ba, suna kafa hujja da Hadisin da Annabi (SAW) ya ce “… kar ku sanya ƙabarina ya zamo wurin idi…”. A tasu fahimtar yin ziyararsa (SAW) koyaushe ya zama kamar Idi. To ba haka malamai suka fassara wannan Hadisin ba.
Ma’anar Hadisin in ji Malamai ita ce “kar a sanya ziyarar ƙabarin ta zama Idi wadda ba za a riƙa yi ba sai shekara-shekara.” Saboda dama Idi ba kullum ake yi ba, don haka Hadisin yana nufin kar a ƙi yin ziyarar har ya zama daga shekara sai shekara. Duk lokacin da aka samu iko a yi kawai.
Haka Malaman da ke da soyayyar Manzon Allah (SAW) a zuciyarsu suka fahimci Hadisin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Idan mai ziyara ya assalamu alaika ya idan mai ziyara ya idan mutum ya yi ya halarto da
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja
Abdulahi, wanda ke jigilar kaya daga Agbara a Jihar Ogun zuwa Ibadan, ya ce yana kashe har Naira 25,000 a kowace tafiya da yake yi, inda mafi yawan kuɗin ke shiga hannun ƴ an Agbero a Legas, waɗanda ke gudanar da ayyukansu sa’o’i 24 a rana, kwana 7 a mako.
Ya ce daga Berger, gefen Legas, zuwa Agbara, manyan motoci kan gamu da aƙalla tashoshi 15 na ta’annati, inda ake karɓar kuɗi tsakanin Naira 1,000 zuwa Naira 3,000 a kowane wuri.
Manajan Daraktan wani kamfani da ke aiki a cibiyar masana’antu ta Agbara a Jihar Ogun, wanda ya nemi a sakaya sunansa ba, ya shaida wa wannan jarida cewa jigilar kwantena na kayayyakin masarufi daga tashar jiragen ruwa ta Apapa a Legas zuwa Agbara na iya kaiwa har Naira 700,000, sakamakon ayyukan waɗannan ƴ an Agbero da ba su da izinin doka.
Babu shakka, waɗannan kuɗaɗen ana sauke su ne kan masu sayen kayayyakin da kamfanonin masana’antu ke samarwa.
Haka nan, fasinjoji na jayayya cewa nauyin kuɗin da aka ɗora wa direbobi a ƙarshe ana sauke shi ne a kan su ta hanyar ƙarin kuɗin haya.
“Kuɗin haya na tashi kullum, kuma wani ɓangare na matsalar waɗannan kuɗaɗen haramtattu ne,” in ji Chidinma Okafor, wata fasinja da ke zama a Legas.Ga wasu direbobi ma, cin zarafin ya wuce batun kuɗi. “Idan ka ƙi biyan kuɗi, za su fasa gilashin motarka ko kuma su cire madubin gefe,” in ji Sani Mohammed, direban Abuja. “Ya zama kamar muna yi musu aiki ne, ba wai don kanmu ba.”
A Fatakwal kuwa, fasinjoji na cewa rashin tsaro na zama babban ƙalubale. “Tashoshin motoci cunkushe suke kuma waɗannan ƴ an Agbero na tsoratar da fasinjoji ma,” in ji wata ɗaliba, Amara Nwankwo.
Ta ƙara da cewa: “Ba ka da tabbacin ko adadin kuɗin da kake biya shikena, ko kuma ana tilasta maka ka biya ƙarin kuɗi.”
A Legas kuwa, matsalar ta fi tsananta. Wani shugaban ƙungiya a Legas, da ya nemi a sakaya sunansa, ya ƙiyasta cewa ƴ an Agbero suna tara sama da Naira biliyan 100 a duk shekara daga harajin da ba na doka ba da suke ƙaƙaba wa direbobi a Legas.
Masu ruwa da tsaki na cewa waɗannan kuɗaɗe ba sa komawa wajen inganta ababen more rayuwa ko samar da ayyuka.
Masana suna gargaɗi cewa ƙara yawaitar wannan rashin gaskiya na da illa ga tattalin arziki da kuma zamantakewa.
“Ayyukan ƴ an Agbero da ba a sarrafa su ba suna hana zuba jari na doka a fannin sufuri, suna ƙara taɓarɓarewar tsaro a tashoshin motoci, sannan suna ƙara tsadar rayuwa ga talakawan ƴ an Nijeriya,” in ji tsohon ƙaramin ministan harkokin sufuri a wani taron masu ruwa da tsaki, Prince Ademola Adegoroye.
“Gwamnati dole ta matsa zuwa ga tsari na doka da kuma inganta tafiyar da harkokin tashoshin mota idan ana son wannan ɓangare ya bayar da gagarumar gudummawa ga tattalin arzikin ƙasa,” in ji Dr. Feliɗ Echekoba, masanin tattalin arziki daga Jami’ar Nnamdi Azikiwe.
Ƙungiyoyin farar hula ma sun yi kira da a yi gyara. Bisa ga Centre for Justice and Peace, wata ƙungiya mai zaman kanta (NGO), tsarin karɓar haraji ta hanyar da ba ta doka ba na rage amincewar jama’a da hana gaskiya ta bayyana a fili.
“Idan hukumomin gwamnati suka ɗauki nauyin karɓar kuɗaɗen kai tsaye, hakan zai rage satar kuɗaɗe, ya inganta gaskiya da riƙon amana, tare da kare direbobi daga cin zarafi da tsangwama a kullum,” in ji ƙungiyar a cikin wata sanarwa.
Kuma jami’an tsaro sun amince cewa tsarin yana jawo ruɗani. “A lokuta da dama muna kama direbobi saboda laifukan hanya, amma idan ka duba sosai, da yawa daga cikinsu waɗanda ne aka zalunta da haraji na ƙarya ne daga hannun ƴ an Agbero,” wani babban jami’in ƴ ansanda a Legas ya shaida wa wakilinmu cikin sirri.
Ya ce wannan shi ne dalilin da ya sa ake yawan ganin tashin hankali a kan tituna.
Ƙungiyoyin direbobi, duk da sun amince da ƙalubalen, sun dage cewa yin doka da tsari kan harkokin ne ya dace fiye da kawar da ayyukansu baki ɗaya.
“Ina buƙatar kulawa ta musamman daga gwamnati domin a tabbatar da cewa an daidaita haraji kuma ana bayar da rasit. Ta haka ne direbobi za su san ainihin abin da suke biya, kuma fasinjoji ba za su ɗauki nauyin biyan kuɗaɗen da ba su dace ba,” in ji Sunday Ogunleye, wakilin ƙungiya a Ota, Jihar Ogun.
Haka kuma, talakawa ma suna bada ra’ayinsu. “Ya kamata gwamnati ta ƙirƙiro tsarin tikitin zamani irin na e-payment a tashoshin motoci, kamar yadda ake da shi a BRT na Legas. Idan aka yi haka, direbobi da fasinjoji za su samu cikakken bayani, kuma babu wanda zai iya karkatar da kuɗi ba bisa ƙa’ida ba,” in ji Maryam Dennis, ma’aikaciyar gwamnati a Fatakwal.
Yayin da al’amarin ke ƙara ta’azzara, ƴ an Nijeriya da dama suna kira ga gwamnati ta tarayya da ta jihohi su ɗauki mataki ta hanyar samar da manufofi bayyanannu, tsarin tikitin zamani, da kuma tsauraran matakai kan karɓar kuɗaɗen haram.
A halin yanzu, direbobi da fasinjoji suna cewa wannan harajin na tilas ya zama abin da suke fuskanta kullum, wanda ke ci gaba da raunana rayuwarsu tare da tsananta matsalar tsadar rayuwa a faɗin ƙasar.
Abuja
Ko’ina ka juya, musamman a tashoshin motoci da aka fi sani a tsakiyar birni da unguwannin FCT, sawa’un direba ne kai ko fasinja, ɗaya daga cikin abubuwan da ake yawan gani shi ne ƴ an Daba, da aka fi sani da ‘Agbero’. Suna tsangwamar masu motoci da suke amfani da hanyoyi, suna karɓar kuɗaɗe Agberon-Agberon ba tare da wani tsari daga hukumomin gwamnati ba.
Ko a Gadar Mabushi, Gadar Baneɗ, shatale-talen Berger, Jabi, Gadar Area 1, Area 3 Junction ko Gwarinpa, yanayin iri ɗaya ne, yayin da ƴ an Agbero ke ci gaba cin karensu ba babbaka. A ƙasar da ke fama da laifuka da matsalolin tsaro irin su sace-sace, ƴ an bindiga, da ta’addanci, yawancin mazauna FCT suna ƙara fuskantar tashin hankali game da tsaron jama’a.
Alal misali, wani mai motar da ke ƙoƙarin ɗaukar abokin aikinsa ko ɗan uwansa a kan hanyarsa ta zuwa aiki ko dawowa daga aiki, yana cikin tsoro na tsangwamar ƴ an ‘Agbero’, waɗanda ke neman “bayanan motoci” ko wasu kuɗaɗen haram kafin a ba shi damar ɗaukar wanda yake so.
Duk abubuwan da suke yi ya saɓa doka, kuma hakan na iya haifar da barazanar da za ta bayu izuwa fashewar tayoyi ko kama mutum ba bisa ƙa’ida ba zuwa “ofishinsu.” Har ma ƴ an Agbero suna da gadarar bincikar direbobi su basu wasu takardu mallakinsu, tikitin biyan kuɗin haraji ko katin shaida kafin su yi tuƙi a kan titunan FCT.
Hatta masu motocin da ba na haya ba na ƙashin kansu ko ma’aikatan gwamnati da ke ƙoƙarin samun na cefane idan za su ɗauki fasinjoji don taimakawa kansu sayen mai ba a barsu a baya ba, saboda ƴ an Agbero na takura musu, suna neman a biya su wasu kuɗaɗe; in ba haka ba, direbobi da motocinsu ba za su bar su su wuce lafiya ba.
Abin lura a nan shi ne, yawancin mazauna na zargin wasu jami’an ƴ ansanda masu karɓar cin hanci da haɗa kai da ƴ an Agbero wajen tsangwamar direbobi yayin da suke aiki ba tare da la’akari da wanda abin ya shafa ba. Ba a cika kama su ba, yayin da duk wani Agbero da aka kama a cikin lokaci kaɗan ƴ ansanda ke sakin sa, wanda hakan ke ƙara ƙarfin gwiwar ayyukansu na miyagun laifuka.
Mummunan Al’amarin da ya afku a Mabushi
Kimanin ƙarfe 1:30 na ranar wata Laraba, 3 ga Satumba, wani mummunan lamari da ya shafi wani iyali ya faru ƙarƙashin gadar Mabushi a Abuja. Wani mutum, mai suna Emeka Ehekweme, tare da matarsa, yana tuƙa wata Toyota Highlander mai launin toka, mai lambar rajista ABJ 206 EC, lokacin da ƴ an Agbero uku da ba a tantance ba suka firgita su da wasu mutane.
Ana zargin cewa ƴ an Agberoran sun tilasta lallai sai sun shiga gaban motarsa, inda ɗaya daga cikinsu ya yi ƙoƙarin kama sitiyarin motar. Sakamakon haka, kan motar ya ƙwace motar ta tafi ta buge wata Mazda da aka ajiye a gefen hanya, ta sake dukan ginin gada sannan ta faɗa rami, hakan ya faru a kan babbar titin Nnamdi Azikiwe.
A cewar mai magana da yawun ƴ ansanda ta FCT, Josephine Adeh, lamarin ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama yayin da direban Highlander, matarsa da wasu biyu daga cikin masu kai farmaki suka rasu a Asibitin ƙasa, yayin da wani wanda ake zargi na uku ke karɓar magani a halin yanzu. Direban Mazda ɗin Suleiman Mohammed, bai ji rauni mai haɗari ga rayuwa ba.
Sakamakon haka, mazauna wurin da suka fusata sun bi ƴ an Agberoran uku, suka kashe su nan take tsaye sannan suka ƙone su. Ana zargin cewa ƴ an Agberoran na daga cikin Abuja Municipal Area Council (AMAC) ne.
Lamarin ya jawo damuwa a bainar jama’a kan ayyukan ƴ an Agbero a Abuja, inda yawancin mazauna ke kiran gwamnati da ta ɗauki mataki na gaggawa don dakile tsangwama a tituna da kuma tsaurara dokokin hanya.
Koke
A yayin da take magana da wakilinmu, wata ma’aikaciyar gwamnati, Ruth Ayodele, ta ce ƴ an Agbero sun mamaye FCT kuma hukumomi ne ya kamata su ɗauki mataki a kansu. Ta yi ƙorafi cewa jami’ai ba sa aikinsu kamar yadda ya kamat.
Ta ce: “Idan aka duba abin da ya faru kwanan nan a Mabushi, inda wasu ma’aurata da wasu Agbero biyu suka rasa rayukansu, abin mamaki ne cewa har yanzu ba a bayar da sanarwar hukuma ta haramta ayyukansu a FCT ba.
“A ƙasa mai aiki haka, irin wannan lamari zai sa a ɗauki mataki cikin gaggawa. Alal misali, Jihar Anambra ta riga ta haramta ayyukan Agbero saboda yadda suke gudanar da ayyukan da suka saɓa wa al’umma.
Gwamnati ta basu damar samun ayyukan yi, matuƙar sun yi rajista da hukumomin ƙananan garuruwa. A bi hanya madaidaciya domin magance matsalar a maimakon a zuba musu ido. Wannan lamari abin takaici ne sosai.”
“Ƴan Agbero suna ko’ina, suna addabar masu motoci. Yanayin na ƙara fitowa daga iko kuma yana buƙatar kulawar gaggawa daga hukumomi domin kauce wa ƙarin asarar rayuka da dukiya, kamar abin da ya faru a Mabushi,” in ji wata ma’aikaciyar gwamnati.
Haka kuma, wani likita, Jacob Nnaemeka, ya ce sau da dama ƴ an Agbero suna tsangwamarsa yayin da yake ɗaukar ko sauke da abokan aikinsa, inda ya buƙaci hukumomin da abin ya shafa su dubi lamarin.
Ya ce: “Kowa ya san cewa ƴ an Agbero na tsangwamar fasinjoji a FCT. Ni ma na ta zama wanda abin ya shafa a lokuta da dama. A wata rana ta musamman, ina son ɗaukar abokin aikina a Area 1. Kafin na yi wata-wata, ƴ an Agbero sun shiga motata sun fara ƙoƙarin cire min makulli. Na tambaye su menene matsalar, sai suka ce ina ɗauka da ajiye da fasinjoji; kuma dole sai na biya su.”
“Bayan na nuna musu katin shaidar PCRC na, sai suka bar ni in tafi tare da neman afuwa. Amma duk haka sai da basu Naira 1,000. Tun daga wannan lokaci, na yi matuƙar taka tsantsan kuma sau da yawa ba na ɗauka ko ajiye abokan aiki, maƙwabta ko ƴ an uwa.
“A kwanakin nan, idan na yanke zan ɗauku abokin aikina sai na yi nisan daga tashar su sannan na tsaya, saboda ko’ina suna nan. Suna da ɗaurin gindi, don haka ne suke nuna halayyar rashin tarbiya.”
Nnaemeka ya ci gaba da cewa: “Ko da ka yi tunanin taimaka wa wani don ka ɗauke shi kyuata ba za ka iya ba saboda tsoron ƴ an Agbero. Yanayin ya wuce gona da iri. Haƙiƙa gaskiya ne cewa wasu jami’an ƴ ansanda na aiki tare da su; in ba haka ba, ba za su yi ƙarfin hali su riƙa takura wa mutane ko’ina a FCT ba.”
“Abin da ya faru a Mabushi bai hana su aiki ba, domin har yanzu suna gudanar da ayyukansu a sassa Agberon-Agberon na birni. Lallai abin takaici ne a FCT; hukumomi dole ne su duba wannan lamari.”
“Suna da iyayen gida”
A yayin da yake magana da Blueprint Weekend, Shugaban Police Reform Secretariat, Farfesa Olu Ogunsakin, ya ce shi ma sau da yawa ƴ an Agbero sun farmake shi a FCT. A cewarsa, suna da masu goya musu baya kuma jami’an ƴ ansanda sun san wannan matsala.
Ya ce: “Zan iya ba ku dalilai da dama kan wannan, amma abu ɗaya da ya kamata ku fahimta shi ne na yi aiki a fannin ƴ ansanda na tsawon shekaru da dama. Ni ba jami’in ƴ ansanda bane, don haka ba zan yi magana kan ayyukansu na gudanarwa ba.
Amma a matsayina na mai gudanarwa, wannan wani abu ne da zan iya gaya muku wanda ba sirri ba ne a gare su.
“Suna sane da wannan, kuma ba zan faɗa muku ko suna aiki a kai ko a’a ba, amma ina tabbatar muku cewa su ne ke da alhakin tsaron FCT kamar yadda suke da alhakin tsaro a ko’ina.”
Ya ƙara da cewa: “Idan kuka tambaye ni ra’ayi na na kaina a matsayin ɗan ƙasa, zan ce dole ne mu duba tsarin da ke cikin FCT. Wannan saboda lokaci-lokaci, ina tuƙa Hiluɗ ko I-Luɗury kamar yadda suke kiransa, kuma ina fuskantar farmaki daga mutane da dama. Suna tambayar bayanai, haƙiƙa, akwai yawan hukumomi Agberon-Agberon, da kayan aiki Agberon-Agberon, waɗanda wataƙila suna da masu goyon baya a wani wuri.”
“Al’amari game da tsaron jama’a abu ne mai matuƙar rikitarwa, musamman ganin abin da na fuskanta. Ba abu ɗaya ne zai iya bayyana ba. Akwai dubban dalilai da za su iya amsa wannan tambaya. Amma a kaina, ina da tabbacin suna aiki a kai.
“Amma ɓangaren gyaran tsari game da haƙƙin mutane, lallai a wannan fannin akwai wasu ƴ an ƙasa na musamman. Ra’ayina shi ne cewa ƴ ansanda dole ne su kasance suna ɗaukar mataki. Muna da kwamishinan FCT, muna da DCP mai kula da ayyuka, kuma muna da sashen gudanarwa, doka za ta iya ɗaukar mataki kan kowa. Idan ka yi magana da ƴ ansanda yanzu cewa za su yi akwai wani aiki na musamman da ake yi wanda ba za su iya tattauna shi ba.”
Hukumar Ƴansanda ta FCT na Kaucewa ba da Bayanai
Duk ƙoƙarin da aka yi don samun martanin Hukumar Ƴansanda ta FCT kan matsalar ƴ an Agbero a FCT ya ci tura, yayin da PRO, Josephine Adeh, ta ƙi amsa tambayoyin da ke neman ra’ayin ƴ ansanda a kai.
Bayan karanta saƙonni da dama da wakilinmu ya aika mata a ranar Talata da safe ta WhatsApp ɗinta da aka sani game da batun, ba ta amsa ba, ko da lokacin da wakilin ya kira ta lokaci-lokaci, ta ƙi amsa kiran, kuma har lokacin rubuta wannan rahoto ba ta ce komai ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp