Isra’ila Ta Kashe ‘Yan jaridar Al Jazeera Biyar A Gaza
Published: 11th, August 2025 GMT
Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta kashe wani fitaccen dan jarida na kafar yada labarai ta Al Jazeera Anas al-Sharif tare da abokan aikinsa hudu a wani hari da ta kai Gaza.
Isra’ila ta zarge shi da kasancewa wani jagora na Hamas sannan ta ce ta hallaka shi saboda irin rahotannin da yake bayarwa masu tsanani daga arewacin Gaza.
Isra’ila ta hari ‘yan jaridar biyar – Anas al-Sharif wanda shi ne fitacce tare da Mohammed Qreiqeh masu aikawa da rahotanni ne sai kuma masu daukar musu hoto Ibrahim Zaher da Mohammed Noufal da kuma Moamen Aliwa wadanda dukkanin su suna aiki ne da kafar ta Al Jazeera.
A lokacin da Isra’ila ta kai musu harin ta sama suna cikin wani tanti ne na ‘yan jarida da ke wajen asibitin al-Shifa a birnin na Gaza.
Isra’ilar ta ce kisan hukunci ne na irin rahotannin da Anas din ya ke aika wa Al Jazeera da ke arewacin Gaza.
Baya haka Isra’ila ta kuma ce dan jaridar wani jigo ne na wani reshe na kungiyar Hamas da ke shirya hare-haren makaman roka da Hamas ke kai mata – zargin da Al Jazeera ta musanta.
A sanarwar da ta fitar rundunar sojin Isra’ilar ta zargi al-Sharif da fakewa a matsayin dan jarida- tana zarginsa da hannu wajen kai mata hare-hare da makaman roka kann fararen hula da sojojinta.
Ta ce a baya ta fitar da wasu bayanan sirri da ke tabbatar da alakarsa da ayyunakn soji na Hamas, ciki har da jerin horon ta’addanci da ya halarta.
Sanarwar ta kara da cewa kafin harin sojin na Isra’ila sun dauki matakai na kauce wa illata farar hulha.
Mako biyu da ya wuce Al Jazeera ta soki rundunar sojojin ta Isra’ila kan abin da ta kira kokarin tunzura masu aika mata da rahotanni a Gaza ciki har da al-Sharif.
Kungiyoyin kare hakkin dan’adam sun ce Isra’ila ta kashe ‚yan jarida sama da dari biyu (200) a Gaza tun daga watan Oktoba na 2023, kan abin da suka ce yunkuri ne na hana bayar da rahotannin zargin cin zarafin da Isra’ila ke yi a Gaza.
Isra’ila dai ta hana ‘yan jarida na waje aikawa da rahotanni a fili daga yankin.
Jim kadan bayan harin ne Isra’ila ta fitar da wata sanarwa da a ciki take tabbatar da kai harin da ta ce ta hallaka Anas al.-Sharif, tana mai cewa wani jagora ne a Hamas.
Rundunar sojin ta Isra’ila ba ta ambaci sauran ‘yan jaridar da ta kashe su tare ba.
Al-Sharif, mai shekara 28, yana rubuta sakonni ne ta shafin X, jim kadan kafin mutuwarsa – inda a ciki yake gargadi kan ruwan bama-bamai da Isra’ila ke yi a birnin na Gaza.
BBC ta ga wasu hotunan bidiyo masu tayar da hankali wadanda kuma ta tabbatar da sahihancinsu, na bayan harin da ya hallaka ‘yan jaridar, inda a ciki ake iya ganin mutane na dauke gawawwakin.
BBC/Hausa
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: yan jaridar Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar
Yau Lahadi al’ummar Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar.
Masu kada kuri’a miliyan takwas ne aka tantance domin kada kuri’a a zaben zagaye na farko da Shugaban kasar mai ci Paul Biya mai shekara 92 dake neman wa’adi na takwas.
A cikin makonni biyu na yakin neman zaben, Shugaba Biya wanda aka dade ba a gan shi a bayyanar jama’a ba ya gudanar da gangami guda daya kacal, a garin Maroua dake yankin Arewa mai Nisa, daya daga cikin yankuna uku na arewa, inda ya sha alwashin magance matsalar tsaro da rashin aikin yi.
A hukumance dai ‘yan takara goma sha biyu ne ke fafatawa a wannan zaben, amma biyu sun janye.
Manyan masu kalubalantar Paul Biya guda biyu a wannan zaben su ne, Issa Tchiroma Bakary, na jam’iyyar CNSF, da Bello Bouba Maïgari, wanda zai iya dogaro da jam’iyyarsa ta (UNDP).
Batun tattalin arziki da rashin aikin yi da matsalar tsaro su ne suka fi mamaye yakin neman zaben.
Mista Biya na Jam’iyyar (RDPC), ya fara mulkin kasar ne tun shekarar 1982.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice October 12, 2025 Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine October 12, 2025 Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Aka Tattauna Batun Falasdinu October 12, 2025 Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh October 12, 2025 China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter A Kasar Habasha October 12, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci