Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-11@12:04:00 GMT

Isra’ila Ta Kashe ‘Yan jaridar Al Jazeera Biyar A Gaza

Published: 11th, August 2025 GMT

Isra’ila Ta Kashe ‘Yan jaridar Al Jazeera Biyar A Gaza

Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta kashe wani fitaccen dan jarida na kafar yada labarai ta Al Jazeera Anas al-Sharif tare da abokan aikinsa hudu a wani hari da ta kai Gaza.

Isra’ila ta zarge shi da kasancewa wani jagora na Hamas sannan ta ce ta hallaka shi saboda irin rahotannin da yake bayarwa masu tsanani daga arewacin Gaza.

Isra’ila ta hari ‘yan jaridar biyar – Anas al-Sharif wanda shi ne fitacce tare da Mohammed Qreiqeh masu aikawa da rahotanni ne sai kuma masu daukar musu hoto Ibrahim Zaher da Mohammed Noufal da kuma Moamen Aliwa wadanda dukkanin su suna aiki ne da kafar ta Al Jazeera.

A lokacin da Isra’ila ta kai musu harin ta sama suna cikin wani tanti ne na ‘yan jarida da ke wajen asibitin al-Shifa a birnin na Gaza.

Isra’ilar ta ce kisan hukunci ne na irin rahotannin da Anas din ya ke aika wa Al Jazeera da ke arewacin Gaza.

Baya haka Isra’ila ta kuma ce dan jaridar wani jigo ne na wani reshe na kungiyar Hamas da ke shirya hare-haren makaman roka da Hamas ke kai mata – zargin da Al Jazeera ta musanta.

A sanarwar da ta fitar rundunar sojin Isra’ilar ta zargi al-Sharif da fakewa a matsayin dan jarida- tana zarginsa da hannu wajen kai mata hare-hare da makaman roka kann fararen hula da sojojinta.

Ta ce a baya ta fitar da wasu bayanan sirri da ke tabbatar da alakarsa da ayyunakn soji na Hamas, ciki har da jerin horon ta’addanci da ya halarta.

Sanarwar ta kara da cewa kafin harin sojin na Isra’ila sun dauki matakai na kauce wa illata farar hulha.

Mako biyu da ya wuce Al Jazeera ta soki rundunar sojojin ta Isra’ila kan abin da ta kira kokarin tunzura masu aika mata da rahotanni a Gaza ciki har da al-Sharif.

Kungiyoyin kare hakkin dan’adam sun ce Isra’ila ta kashe ‚yan jarida sama da dari biyu (200) a Gaza tun daga watan Oktoba na 2023, kan abin da suka ce yunkuri ne na hana bayar da rahotannin zargin cin zarafin da Isra’ila ke yi a Gaza.

Isra’ila dai ta hana ‘yan jarida na waje aikawa da rahotanni a fili daga yankin.

Jim kadan bayan harin ne Isra’ila ta fitar da wata sanarwa da a ciki take tabbatar da kai harin da ta ce ta hallaka Anas al.-Sharif, tana mai cewa wani jagora ne a Hamas.

Rundunar sojin ta Isra’ila ba ta ambaci sauran ‘yan jaridar da ta kashe su tare ba.

Al-Sharif, mai shekara 28, yana rubuta sakonni ne ta shafin X, jim kadan kafin mutuwarsa – inda a ciki yake gargadi kan ruwan bama-bamai da Isra’ila ke yi a birnin na Gaza.

BBC ta ga wasu hotunan bidiyo masu tayar da hankali wadanda kuma ta tabbatar da sahihancinsu, na bayan harin da ya hallaka ‘yan jaridar, inda a ciki ake iya ganin mutane na dauke gawawwakin.

BBC/Hausa

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: yan jaridar Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza

Sojojin mamayar Isra’ila sun harba wata mugunyar ‘karfin wuta’ da jiragen saman yaki kan yankin kudancin Gaza

Bayan tsakar dare ne jiragen yakin sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kaddamar da luguden wuta a kudancin birnin Gaza.

Cibiyar yada labaran Falasdinu ta nakalto majiyoyin da ta bayyana a matsayin na cikin gida na cewa: Jiragen saman sojin mamayar Isra’ila sun kaddamar da hare-haren wuce gona da iri, inda suka harba makamai masu linzami sama da 20 cikin ‘yan mintuna a kudancin mahadar Al-Musalaba da Dawla da kuma kusa da masallacin Ali, inda suka nufi kudu.

Wakilin cibiyar ya ruwaito cewa, galibin hare-haren sun fi karkata ne a kan titin 8 da ke kudancin Gaza.

Wadannan hare-haren dai na zuwa ne a daidai lokacin da barazanar da sojojin mamaya ke yi na kaddamar da wani gagarumin farmaki a kan birnin na Gaza ke kara ta’azzara, da nufin kwace iko da birnin da kuma raba mazauna birnin da tilastawa kauracewa gidajensu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar ‘Yan Sahayoniyya Kan Gaza August 11, 2025 Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza August 11, 2025 Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Harin Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza August 11, 2025 Iran: Ba a yanke wani abu game da tattaunawa da Washington ba August 11, 2025 Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza August 11, 2025 Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari August 11, 2025 Chadi: An Daure Wani Dan Adawa Shekaru 20 A Gidan Kaso Da tara August 10, 2025 Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin August 10, 2025 Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasus Ko Rasha Bata taimaka ba August 10, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza
  • Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Wani Hari Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza
  • Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • Ana Alhinin Tunawa Da Harin Nukiliyar Nagasaki Shekarau 80 Da Suka Gabata A Japan
  • Guterres: Dole Ne Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ta Gaggauta Janye Shirinta Kan Gaza
  • Kasashen Larabawa Da Kungiyoyinsu Sun Yiu Allah Wadai Da Shirin ‘Yan Shayoniyya Kan Gaza
  • Jamus ta dakatar da ba wa Isra’ila kayayyakin aikin soji saboda shirinta na mamaye Gaza