Aminiya:
2025-09-24@11:17:39 GMT

Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh

Published: 9th, August 2025 GMT

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga jama’a da Gwamnatin Jihar Binuwai bisa rasuwar Cif Audu Ogbe tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Cif Audu Ogbeh.

Ya kuma yi wa iyalansa, abokansa da dukkanin ’yan uwansa ta’aziyya kan rashin da suka yi.

Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfara  Tsohon Ministan Noma Audu Ogbeh ya rasu

Cif Ogbeh, ya rasu yana da shekaru 78 a duniya, ya hidimta wa Najeriya a ɓangarori daban-daban ciki har da Ministan Sadarwa a lokacin Jamhuriya ta Biyu.

Sannan daga baya ya zama Ministan Noma a Gwamnatin marigayi Muhammadu Buhari.

A cewar sanarwar Bayo Onanuga, mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labaru, Ogbeh mutum ne mai basira da zurfin tunani wanda ya taimaka wajen tsara manufofin gwamnati da magance manyan matsalolin ƙasa.

Ogbeh, ya fara harkar siyasa a shekarun 1970 a matsayin ɗan majalisa, sannan daga baya ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa jam’iyyar APC.

Shugaba Tinubu, ya bayyana shi a matsayin “Ɗan ƙasa wanda hikimarsa, jajircewarsa, da ƙoƙarinsa na ci gaba suka bar tarihi a siyasar Najeriya.

“Kullum yana da hujjoji da alkaluma don kare ra’ayinsa. Ƙasa za ta yi matuƙar kewar gogewarsa.”

Shugaban ya yi addu’ar Allah Ya jiƙansa ya kuma bai wa iyalansa haƙuri da juriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: rasuwa ta aziyya

এছাড়াও পড়ুন:

An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno

Wata Kotun Soji ta yanke wa wasu sojoji uku hukuncin ɗaurin rai da rai kan sayar da makamai da harsasai ba bisa ka’ida ba a Maiduguri, Jihar Borno.

Kotun sojin ƙarƙashin jagorancin Birgediya-Janar Mohammed Abdullahi, ta bayyana cewa an yanke wa mutum uku daga cikin sojojin huɗu hukuncin ɗaurin rai da rai yayin da aka ɗaure mutum ɗaya shekaru 15 a gidan yari.

Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa Yarima Salman ya jagoranci jana’izar babban mai ba da fatawa na Saudiyya

Sojojin da abin ya shafa sun haɗa da Raphael Ameh da Ejiga Musa masu muƙamin sajan, da kuma Patrick Ocheje mai muƙamin kofura.

Binciken kotun ya nuna cewa Ameh ya karɓi sama da ₦500,000 daga harƙallar sayar da harsasai kafin daga bisani a kama shi yana ƙoƙarin sayar da wasu ƙarin makaman.

Da yake yanke hukunci, Janar Abdullahi ya bayyana su a matsayin “ƙwayaye bara-gurbi” da suka ci amanar rundunar soji, suka karya ƙa’idar ladabi da biyayya, tare da wulaƙanta mutuncin da ake tsammani daga jami’an soja a yaƙin da ake yi da ta’addanci.

Bayanai sun ce wannan hukuncin na zuwa ne bayan amincewar su kan aikata laifuffukan da suka haɗa da “sata da cinikin makamai ba bisa ka’ida ba, da taimaka wa maƙiya” wanda duka laifuka ne ƙarƙashin dokar sojojin Najeriya.

Kotun ta bayyana cewa “irin wannan safarar da ba bisa ƙa’ida ba na zama haɗari ga sojoji da ayyukansu, da kuma tsaron ƙasa, don haka yana nufin taimaka wa maƙiyan ƙasar.”

Shugaban Kotun, Brigadier Janar Abdullahi, ya ce waɗannan laifuka da sojojin suka aikata ba matsala ce kawai ta karya doka ba, har ma da cin amana, da martabar da ake sa ran sojoji su riƙe.

Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa ba za ta lamunci irin waɗannan rashin ɗa’a da halayen damfara ko rashin ƙwarewa ba.

Babu shakka Jihar Borno ce cibiyar rikicin Boko Haram a Najeriya wadda ta kwashe kimanin shekara 15 tana fama da shi, lamarin da ya laƙume rayukan dubban mutane da haifar da matsalar jin-ƙai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNGA: Yau Shettima zai gabatar da jawabin Najeriya a MDD
  • An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh ya rasu yana da shekara 82
  • Faransa ta amince da ’yancin ƙasar Falasɗinu a hukumance
  • Sarkin Ruman Katsina ya rasu
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa
  • Ministan Harkokin Waken Falasdinu Ta Yi Kira Ga Karin Kasashe Su Amince Da Samuwar Kasarta
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila
  • SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook