Aminiya:
2025-08-09@13:30:06 GMT

Fashewar gurneti ya kashe yara uku a Borno 

Published: 9th, August 2025 GMT

Fashewar gurneti ya salwantar da rayukan yara mata uku a garin Pulka da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza a Jihar Borno.

A wani rahoto da ma’aikacin Sibiliyan JTF Buba Yaga ya fitar, ya ce ɗaya daga cikin ƙananna yaran suna wasa da gurnetin da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne, suka yi watsi da su a lokacin da gurnetin ya tashi da misalin ƙarfe 2:20 na ranar Alhamis.

An garzaya da yaran zuwa Babban Asibitin Gwoza, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.

Daga nan ne aka miqa gawarsu ga iyalansu domin yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja

Haɗaɗɗiyar tawagar ’yan sandan da suke tantance bama-bamai (EOD-CBRN), da dakarun Operation Hadin Kai, CJTF, da mafarautan yankin sun ziyarci wurin, inda suka gudanar da aikin share wasu na’urori.

Ba a samu ƙarin ko ɗaya ba, kuma an ayyana yankin a matsayin keɓantaccen wurin da za a kauce wa bi zuwa wani lokaci.

Hukumomin tsaron sun bukaci mazauna yankin da su gaggauta kai rahoton abubuwan da suke zargi ga jami’an tsaro domin hana afkuwar irin wannan bala’i.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram yara

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano

Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Wakilai, Abubakar Kabir Abubakar, ya ce Gwamnatin Tarayya za ta kashe Naira tiriliyan daya da rabi don gina layin dogo na zamani domin saukaka harkar sufuri a cikin birnin Kano.

Ya bayyana hakan ne lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a Kano, inda ya ce aikin zai saukaka wa mazauna birnin wahalar da suke sha a harkar sufuri.

Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano

Ya ce, “Wannan aikin na gina layin dogo na zamani ya kai Dalar Amurka biliyan daya, kwatankwacin Naira tiriliyan daya da rabi.

“Ga wadanda suke tafiye-tafiye zuwa kasashen waje, musamman kasashen Turai da nahiyar Asiya, sun san akwai irin wadannan ayyukan kuma suna da muhimmanci. Aikin zai kara habaka tattalin arzikin jihar idan aka kammala shi.”

Dan majalisar ya kuma ce sabanin yadda ake yadawa, Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya bullo da muhimman ayyukan raya kasa a bangarorin lafiya da aikin gona da ilimi da kuma tsaro a Arewacin Najeriya.

“Abin mamaki ne idan na ji wasu mutane na cewa Shugaba Tinubu bai damu da Arewa ba. Ni ne shugaban kwamitin kasafin kudi, kuma na san me ya yi wa Arewa.

“Ya kamata mu ajiye son rai a gefe guda mu fada wa kanmu gaskiya a kan Shugaba Tinubu. Ya bijiro da ayyuka da dama a Arewa da ya kamata a yaba masa,” in ji Abubakar Bichi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja
  • An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
  • Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno
  • Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno
  • Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano
  • UNICEF Ya Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara Sama Da 17,000 A Kano
  • ‘Hayakin janareta’ ya kashe mutum 4 ’yan gida daya a Borno
  • Ma’aikatan gwamnati na amfani da kudaden sata wajen gina rukunin gidaje – EFCC