Aminiya:
2025-08-09@15:56:19 GMT

Tsohon Ministan Noma Audu Ogbeh ya rasu

Published: 9th, August 2025 GMT

Allah Ya yi wa tsohon Ministan Aikin Gona, Cif Audu Ogbeh rasuwa.

Iyalansa sun sanar cewa a safiyar Asabar Allah Ya yi masa cikawa, yana da shekara 78 a duniya.

.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ya rasu

এছাড়াও পড়ুন:

Mahaifin Ɗan Bello ya rasu

Fitaccen matashin nan mai barkwanci, Bello Habib Galadanci, wanda aka fi sani da Ɗan Bello, ya yi rashin mahaifinsa a yammacin wannan Alhamis din.

Matashin lauyan nan ɗan gwagwarmaya, Abba Hikima, ne ya bayyana hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026

“Innalillahi wa inna IlaiHi rajiun. Allah Ya yi wa Mahaifin Dokta Bello Galadanchi (Dan Bello) rasuwa yanzun nan. Allah Ya gafarta masa. Ameen,” a cewar saƙon da Abba Hikima ya wallafa.

Kawo yanzu dai ba a bayyana dalilin rasuwar mahaifin Ɗan Bellon ba, amma wasu kafofin watsa labarai sun ruwaito cewa marigayi ya rasu bayan fama da jinya.

Ɗan Bello ya kasance dan gwagwarmaya marar tsoro da ake ganin na daga cikin matasa da za su iya kawo sauyi a ƙasar nan.

Matashin ya sha ƙalubalantar gwamnatocin jihohi har ma da tarayya kan sakaci da walwalar al’ummar da suke jagoranta musamman a bangaren ilimi da kuma harkokin lafiya domin zaburar da su kan abin da ya kamata.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Hukumar Tsaron Farin Kaya DSS ta riƙe matashin na dan lokaci taƙaitacce yayin saukarsa a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano bayan shigowarsa ƙasar daga China.

Ɗan Bello dai ya yi ƙaurin suna wajen yin bidiyon barkwanci kan matsalolin shugabanci da cin hanci a Nijeriya.

A kwanan baya wasu saƙonni da ya wallafa kan matsalar fanshon ’yan sanda da ta matsalar albashin malaman jami’a sun ɗauki hankali matuƙa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh
  • Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
  • Kasashen Larabawa Da Kungiyoyinsu Sun Yiu Allah Wadai Da Shirin ‘Yan Shayoniyya Kan Gaza
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
  • Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
  • Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
  • Mahaifin Ɗan Bello ya rasu
  • Al’ummar Zamfara: ’Yan bindiga sun karɓi N56m domin izinin yin noma
  • Ministan tsaron Ghana da wasu sun rasu a hatsarin jirgin sama