Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargin ’yan kungiyar asiri ne tare da kwato musu wasu abubuwa na bata gari a Ilorin.

 

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, Adetoun Ejinre-Adeyemi ya fitar, ya ce, ‘yan sandan da ke aiki bisa sahihiyar bayanan sirri daga majiyoyin tsaron al’umma, sun dauki wami mataki kan wani harin fashi da makami da ya afku a wani dakin kwanan dalibai da ke unguwar Eleko, Ilorin.

Sanarwar ta ce ba tare da bata lokaci ba jami’an ‘yan sanda da ‘yan banga, sun kai ga kama wasu maza biyu da ake zargi.

 

Ta ce wadanda ake zargin sun hada da Ishola Adeyemi, da Ismail Rafiu dukkansu na Ibadan, jihar Oyo.

 

A cewarsa yayin da ake yi musu tambayoyi na farko, wadanda ake zargin sun amsa cewa wani Qudus mai suna “Tiny”, memba ne na kungiyar Ido Cult Fraternity, ya gayyace su zuwa Ilorin don kawar da wani dan kungiyar asiri.

 

Ya yi nuni da cewa, a lokacin da harin nasu bai yi nasara ba, sai suka koma yin fashi a gidajen kwanan dalibai a yankin.

 

Ya yi bayanin cewa wadanda ake zargin, tare da baje kolin da aka kwato an mika su zuwa Sashen Yaki da Fashi, Sashen Binciken Laifukan Jiha (SCID), hedikwatar Jiha, don ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a gaban kotu.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi

Gwamnatin jihar Kano ta amince da korar wasu manyan mataimaka na musamman (SSAs) ba tare da bata lokaci ba, sakamakon zarge-zargen da wasu kwamitocin bincike suka yi na gudanar da bincike kan wasu laifuka.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Alhaji Umar Farouk Ibrahim ya fitar.

 

A wani gagarumin mataki da gwamnan ya dauka, ya amince da korar Abubakar Umar Sharada, babban mataimaki na musamman kan harkokin siyasa, bayan da kwamitin bincike na musamman ya tuhume shi a matsayin wanda ya shirya belin wani mai hatsarin gaske kuma dilan kwyaan maye, Sulaiman Aminu Danwawu, wanda ya tabbatar da laifin Abubakar Sharada a cikin takaddamar belin ta hanyar kwamitin da ya gabatar a gaban kwamitin.

 

A cewar wata wasika da ya fitar a ranar Juma’a, 8 ga watan Agusta 2025, ta hannun sakataren gwamnatin jihar (SSG), Sharada an umurce shi da ya mika dukkan kadarorin gwamnati da ke hannun sa ga babban sakatare, bincike, ranar Litinin, 11 ga Agusta 2025.

 

An kuma gargade shi da kada ya nuna kansa a matsayin jami’in gwamnati a wannan gwamnati mai ci.

 

Hakazalika, gwamnan ya sauke Tasiu Adamu Al’amin Roba, babban mataimaki na musamman, daga mukaminsa bayan kama shi da laifin sama da fadi da wasu buhunan hatsi a wani dakin ajiyar kaya da ke Sharada a shekarar 2024.

 

Tuni dai Roba ya gurfana a gaban kotu inda ake tuhumarsa da laifin sata da hada baki a kan zargin karkatar da kadarorin jama’a.

 

Haka kuma an umurci Tasiu Adamu Al’amin Roba da ya mika dukkan kadarorin gwamnati da ke hannun sa da suka hada da katin shaida a ranar Litinin ko kuma kafin ranar Litinin 11 ga watan Agusta 2025. Ya kuma yi gargadin kada ya bayyana kansa a matsayin ma’aikacin gwamnati a wannan gwamnati mai ci.

 

A wani labarin kuma, gwamnatin jihar ta wanke Hon. Musa Ado Tsamiya, mai ba shi shawara na musamman kan magudanun ruwa, wanda kwamitin bincike ya wanke shi daga dukkan zarge-zargen, inda ya tabbatar da cewa ba shi da laifi.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatin sa na tabbatar da adalci da kuma rashin hakuri da cin hanci da rashawa, yana mai gargadin dukkanin jami’an gwamnati da su kasance masu bin ka’ida mai inganci a ayyukansu da kuma rayuwarsu ta sirri.

 

A cikin wannan sanarwa, ana shawartar jama’a da kada su yi wata hulda da wadannan ‘yan siyasa biyu da aka kora a kan duk wani batu da ya shafi gwamnatin jihar Kano, duk wanda ya yi haka, ya yi ne a kan kansa.

 

 

 

Saki/Abdullahi jalaluddeen/Kano

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato Tambuwal kan zargin N189bn
  • An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • An Yi Allah Wadai Da Hana Amfani Da Hijabi A Jami’ar LandMark, Omu-Aran Kwara
  • Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila
  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi