Ana Zanga-Zanga A Isra’ila Kan Shirin Netanyahu Na Mamaye Gaza
Published: 10th, August 2025 GMT
Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra’ila, don adawa da matakin gwamnatin ƙasar na faɗaɗa farmakin sojin da take a Gaza.
A ranar Juma’a ne majalisar tsaron Isra’ila ta amince da sharuɗa biyar na kawo karshen yaƙin, ciki har da shirin karɓe iko da Birnin Gaza, inda sojojin Isra’ilar suka ce za su “shirya karɓe iko” da Gaza baki ɗayanta.
Masu zanga-zangar da suka haɗa da iyalan mutum 50 ɗin da ake garkuwa da su a Gaza – ciki har da 20 ɗin da ake kyautata zaton suna raye, suna fargabar cewa shirin zai saka rayuwar ƴan uwansu cikin haɗari, inda suka buƙaci gwamnatin Isra’ila da ta yi ƙoƙarin don ganin an sake su.
Shugabannin Isra’ila sun yi watsi da sukar da ake yi wa shirinsu, inda Firaminista Benjamin Netanyahu ya ce “hakan zai taimaka a saki mutanen mu”.
Wata ƙungiya da ke wakiltar iyalan waɗanda ake garkuwa da su ta wallafa a shafin X cewa: “Faɗaɗa farmakin zai saka mutanen mu da kuma sojoji cikin barazana – al’ummar Isra’ila ba su da niyyar saka su cikin haɗari”.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Axios: Majalisar ministocin Isra’ila ta amince da sabon shiri na mamaye birnin Gaza
Majalisar ministocin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta amince da kudirin firaminista Benjamin Netanyahu na mamaye birnin Gaza, wanda ke zama matakin farko na wani gagarumin farmakin soji da ka iya kaiwa ga mamaye daukacin zirin Gaza, a cewar wani babban jami’in Isra’ila.
Matakin ya biyo bayan tattaunawa sama da sa’o’i 10 da aka shafe ana yi tare da nuna wani gagarumin shiri na ci gaba da kai hare-haren Isra’ila kan Gaza.
Jami’an Amurka sun ce shugaba Trump ya zabi kada ya shiga cikin lamarin, inda ya zabi barin Isra’ila ta yanke shawarar kanta.
A wani bangare na sabon farmakin da ke tafe, ana sa ran dakarun haramtacciyar kasar Isra’ila (IOF) za su ba da umarnin kwashe Falasdinawa kimanin miliyan 1 da ke zaune a birnin Gaza da yankunan da ke kewaye da su a halin yanzu.
A cikin wata sanarwa, ofishin Netanyahu ya bayyana cewa IOF za ta mallaki birnin Gaza, yayin ake ci gaba da fuskantar matsalar jin kai da Rashin abinci da Ruwan sha gami da maguguna da sauran kayayyakin bukatar rayuwa a dauakcin yankin zirin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Kira taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi August 8, 2025 Iraniyawa Miliyon 1.2 Ne Suka Shiga Iraki Ta Kofar Shiga Na Mehran August 8, 2025 Ansarullah Ta Yi Gargadi Ga Amurka Da HKI Kan Kara Tada Hankali A Yakin August 8, 2025 Hizbullah Da Amal Sun Yi Tir da Shirin Kwance Damarar Hizbullah August 8, 2025 Jirgin Daukar Marasa Lafiya Ya fadi A kasar kenya Ya Kuma Kashe Akalla mutane 6 August 8, 2025 Araqchi: Hari Kan Cibiyoyin Makamashin Nukiliyar Kasar Iran Ba Zai Taba Canza Matsayinta Ba August 7, 2025 Manjo Janar Mousawi: Martanin Iran Nan Gaba Zai Kasance Mafi Muni Kan Makiya August 7, 2025 Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Jaddada Shirinsu Na Tunkarar Duk Wata Barazana August 7, 2025 Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Gaza Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa August 7, 2025 Human Rights Watch Ta Ce: Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Rusa Makarantu Fiye Da 500 A Gaza August 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci