Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro
Published: 8th, August 2025 GMT
Nijeriya ta kasance ƙasa ce, mai girman gaske, wadda kuma ‘yan ta’adda masu iƙirarin jihadi, Al-kamar irinsu; Al- Ƙaeda da ISIS da ke aikata ayyukan ta’addancinsu a yankin Sahel ke kutsowa cikin ƙasar, domin aikata ta’addanci.
Bugu da ƙari, ba tun yau ne, wasu ƙwararru a ɓangaren tsaro na ƙasar nan, suke yin gargaɗin cewa, yadda aka bar iyakokin ƙasar sakakai ne, ke ƙara ta’azzara matsalar tsaro a ƙasa, inda wasu’yan ta’adda daga wajen ƙasar, ke yin amfani da damar, wajen shigowa tare da kuma shigo da muggan makamai da yadda masu ra’ayin riƙau na addini, daga ƙasashe kamar su, Mali da Jamhuriyar Nijar da Chadi, ke shigowa ƙasar, su kuma ci Karensu ba babbaka.
Misali, ‘yan ta’addar ƙungiyar Lakurawa, masu iƙirarin jihadi, waɗanda ta hanyar ayyukan ta’addacin su, suka hana wasu yankuna musamman a Arewa Maso Yamma sakat, daga nan kuma suka ƙara faɗaɗa ta’addacinsu, zuwa wasu yankuna na Arewa Maso Gabas da kuma zuwa iyakokin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar.
Hakazalika, wasu rahotanni sun nuna cewa, ‘yan ta’addar Lakurawan ‘yan aware nada alaka da ƙungiyar masu iƙirarin jihadi da ke gudanar da ayyukansu na ta’addanci, a yankin Sahel, waɗanda shigarwarsu wasu yankuna na Arewa Maso Yammacin ƙasar nan, suka samu damar janyo suke janyo ra’ayoyin wasu matasa cikin ƙungiyar da kuma auren wasu da yankunan na Arewa Maso Yamma.
Shi ma wani tsohon mai magana da yawun rundunar tsaron ƙasar Majo Janar Edward Buba, ya sanar da cewa, ƙungiyar ce, ta ƙara haifar da rudanin siyasa a ƙasashen Mali da Jamhuriyyar Nijar.
Kamar yadda Janar Musa ya faɗa, katange iyakon Nijeriya abu da ke da alfanu da dama ga ƙasar, musamman domin ci gaba da dorewar ƙasar da kuma kare ta, daga hare-hare daga ketare.
Tabbas batun Katange ƙasar, abu ne, da zai laƙumi ɗimbin kuɗaɗe, amma aiwatar da hakan, zai kare Nijeriya daga kutsen ‘yan ta’adda daga wajen aasar.
A wani rahoto da Asusun da ke tallawa kananan yara na majalisar dinkin duniya wato UNICEF, ya yi gargaɗin cewa, rikice-rikicen da ke aukuwa a yankin Sahel ta tsakiya, na kutsawa zuwa wasu ƙasashen da ke maƙwabtaka na yankin, wanda hakan ke kara ta’azzara tarwatsa alumomi daga yankunan su da haifar da matsin tattalin arziki da kuma haifar da karanci kuɗaɗe.
Duba da yadda iyakokin Nijeriya suke sakakai, wannan matsalar za iya cewa, tamkar kasar, na zaune, a karkashin Bam.
Ya zama wajibi mahukunta a Nijeriya su ɗauki dabaru Nijeriya wajen daƙile shigowar ‘yan ta’adda cikin ƙasar.
Duk da cewar, katange iyakon Nijeriya ba zai hana kutsowar ‘yan ta’adda ba, amma katangewar, za ta taimaka wa hukumomin tsaron ƙasar wajen ƙaukar matakan gaggawa na mayar da martani, ta hanyar yin amfani da kayan aiki na sanya ido.
Tsawon iyakonin Nijeriya, ya kai sama da kilomita 4,000 kilomita, wanda hakan ke nuna cewa, sun fi ƙarfin jami’an hukumar kula da shige da fice, iya kula da iyakokin su kaɗai.
Hakazalika, salon shugabanci a ƙasar na rashin nuna damuwa, ya sanya iyakokin ƙasar sun kasance wajen na samun damar shigowar ɓata gari cikin ƙasar, musamman ga ‘yan ta’addar daga yankin Sahel.
Akwai wasu dabarun zamani da ya kamata a runguma a ƙasa na katange iyakokin ƙasar.
Alamisali, ƙasar Fakistan wadda ta yi iyaka da ƙasar Afghanistan, kusan ta kammala katange iyakokinta masu tsawon kilomita 2,611 wanda aikin ya kai kaso 98.
Kazalika, ƙasar Saudi Arabiya, wadda ta yi iyaka da ƙasar Iraki, ta katange iyakar da ƙasar tsawon kilomita 900 domin daƙile shigowar masu fasakwari da kuma barazanar ‘yan ta’adda.
Wadannan misalan kaɗai, sun isa hujjar da nuna cewa, katange iyakokin ƙasa tare da yin amfani da kayan fasahar zamani, za su taimaka wajen ƙara tabbatar ƙasa.
Batun gaskiya a nan shi ne, mun yi ammanar cewar cewa, rashin tsaron da ke ci gaba da addabar Nijeriya ba daga cikin gida Nijeriya ba ne, daga ƙetare ne.
A ra’ayin wannan Jaridar, muma muna goyon bayan kiran na Janar Musa, na buƙatar a katange iyakokin ƙasa, domin kuwa, bai kamata ace, Nijeriya ta yi wani jinkirin aiwatar da hakan ba. Wannan ne matsayar mu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijeriya katange iyakokin a yankin Sahel iyakokin ƙasa a Arewa Maso yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata
Wannan yana faruwa sosai gaskiya, kuma ƙarshe ba a wayewa da lafiya gaskiya. Masu yi gaskiya tun wuri su daina wallahi, dan aure ya sha mutuwa ta sanadin haka ƙarshe azo ana nadama mara amfani. Sosai ana samun gagarumar matsala tsakanin ma’aurata zargi ya shiga tsakani, daga nan ma dai wani aure ka ji ya mutu. Su yi wa kansu faɗa, su daina gaskiya.
Sunana Haj. Maryama Ahmad, daga Jihar Kaduna:
Wannan matsaloli suna faruwa sosai, kuma rashin tunani ne yake janyo hakan. Dalili kuwa ko da namiji ba shi da wannan tunanin na soyayya da wata to, kin ƙirƙirar masa ke da kanka, kin riga da kin nemo masa hanyar da zai riƙa samun damar bibiyar wasu. Haka lambar da za ki ara ko da ace ita macen ba ta bibiye shi ba, watarana zai ji yana son bibiyar lambar musamman lokacin da ki ka ɓata masa, sharrin ɗa namiji na da yawa ya san hanyoyin da dama waɗanda zai bi ya tursasa ita wannan me lambar ko da kuwa ba ta buƙatar sauraronshi har sai ya cimma burinshi. Kin ga kenan kin kawo wa kanki da kanki wata masifar kuna zaune lafiya ke da mijinki, Allah dai ya kyauta. Wannan darasi ne babba musamman ga ƴ an’uwa mata manya da yara, dan wata babbar kamar ƙaramar yarinya haka take. Allah ya sa mu dace.
Sunana Fadila Lamiɗo daga Jihar Kaduna:
In ban da ganganci akan wani dalili za ki ɗauki ‘number’ mijinki ki saka a wayar wata? wannan tamkar bawa mage ajiyar kifi ne, idan ma kina tunanin kin goge ‘number’ bayan kin gama ne shi mijin naki yau da gobe kina masa haka zai iya bin bayan ‘number’ don shi ba walliyi bane, garin neman gira sai a rasa ido. Ina kira ga mata su guji tsananta buncike, su sa a zuciyarsu kishiya ƙaddara ce kuma bawa baya iya gujewa ƙaddararsa. Su mayar da hankali wajen roƙon Allah abin da suke so wa kan su na alheri, in sha Allahu Allah zai shiga cikin lamarinsu, ba tare da sun ɗaga wa kansu hankali ba, wajen binciko abin da ka iya kawo masu rashin kwanciyar hankali.
Sunana Princess Fatimah Mazadu, daga Jihar Gomben Nigeria:
Tirƙashi kin san wauta da dolanci wallahi wannan shi ne, kat! ah to, in ba wauta ba ke kin isa ki gama sanin ɗa namiji? Ko chat da neman hanyoyi ta zamani za ta isar miki ki gane halayen mijinki ko sanin ƴ an matanshi ko neman aurenshi da makamantansu?. Ai tonon asiri ne da rashin sanin zafin kai, da ƙoƙarin saka zargi tsakanin zamantakewarku. Ai kira da babbar murya in har akwai masu niyyya ma wallahi kar su kuskura, dan wata in ta yi ta wanye lafiya, wata gidansu za a korata. Shurme ne sosai ace wai mace tana bibiyar namiji akan dole ta san ainihin abun da ke tafiya a rayuwarshi, an ce mana mazan daƙiƙai ne? ai sun fi mu wayewa a wannan fannin. Tunda dai ban taɓa jin an ce ga mace ta ƙirƙiri Tiktok ko Facebook ko Instagram ba, kawai ki kasance mai yadda da shi akowani hali idan bai saɓawa addininmu. Matsaloli kam, ai ba adadi dan garin gwadashi wallahi za ki gwado bala’i a ƙoƙarinki na ki san meke tafiya, kawai ana cikin hira ya ce misali “yau ina komawa ma zan saki matata tun da zan mallakeki…” Dan Allah ya za ki yi? Shin za ki tonawa kanki asiri ne, ko za ki cigaba da chat ɗin?, ko daga ya dawo za ki tare shi?, ko za ki hau haɗa kayanki ne?, kin ga wannan ƙaramin misali ne, wallahi mata su kiyayye wannan shurme ne. Matsaloli kamar; rashin kwanciyar hankali, zargin juna, nadama, da-na-sani, banzar aƙida.
Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Rano LGA Jihar Kano:
Idan za a yi ba mai zurfi ba, kuma za a yi gwajin da zuciya ɗaya bada niyyar tayar da fitina ba a nawa fahimtar babu matsala. Akwaisu matsaloli kam, idan har ita cen ta fiye gwajin mai zurfi. Shawarata a nan ita ce, kawai duk wata mace tana yi wa mijinta kyakykyawan zato musamman akan ƙarin aure, domin Allah ne da kansa ya halastawa namiji ya auri mace har guda huɗu amma fa idan zai yi adalci, shi kuma adalci ubangijinmu ne kaɗai mai yinsa daidai. Allah kasa mu dace amin.
Sunana Hadiza Ibrahim D. Auta, Ɗaura-Namoda Jihar Zamfara:
Babban ƙalubale ne ga mata masu irin wannan halin bin diddigi, ko ga namiji ballantana ga mace wadda ba ta isa ta saka ko ta hana ba. Kira na ga masu irin wannan halin su daina gwajin su tsayar da hankalinsu a kan abin da suka gani zahiri. Saboda Allah da kansa ma ya ce kada mu tsananta bincike, gudun garin tone-tone kaza ta tono wuƙar yanka ta. Akwai illoli masu tarin yawa dangane da matsalolin da wannan gwajin yake haifarwa ga masu riƙo da shi a matsayin wayewa, ko babban makamin da suke riƙo da shi domin tabbatar ko gano; ana son su ko ba a son su, kuma mijinsu yana kula wasu matan ko babu ruwansa da su. Saboda ba a gwada namiji da mace komai muninta. Don akwai wata da ta taɓa saka ƙawarta ta yi wa saurayinta gwajin; daga haka aure ya ƙullu a tsakaninsu ya bar budurwarsa ta asali ya auri ƙawarta. Haka ma ƙawa ta taɓa kwace mijin ƙawarta a irin wannan gwajin daga wasa. Shawarata ga masu yi kawai su daina, a wannan zamanin da muke ciki miji ko saurayi duka ɓoye su ake yi kamar an samu kuɗi. Wata ko ba a saka ta yin gwajin ba gaban kanta take yi, idan ta samu dama sai dai ƙawar ta ji labari a sama zancen ya sauya, mai son ta ya koma kan ƙawarta ko kuma ƙawarta za ta aure mata miji.
Sunana Muktari Sabo, Jahun A Jihar Jigawa:
Mata mutanenmu lallai hakan tana faruwa wato mace take bibiyar mijinta ta hanyoyi mabambanta ciki kuma har ta waya. Kiran da zan yi akan haka shi ne, mata su ji tsoron Allah kuma su sani bibiyar ba abin da za ta hana wanda Allah ya sa zai faru. Akwai matsaloli; na farko dai ta ɗorawa kanta rashin kwanciyar hankali, sannan hakan zai iya haifar mata matsala tsakaninta da mijinta. Shawara a nan ita ce mata masu wannan hali su daina, domin yin hakan ba zai hana ayi musu abin da suke tsoro ba wato kishiya.
Sunana Hafsat Sa’eed, daga Jihar Neja:
A nawa tunanin hakan bai kamata ba, mace ta gwada kiran mijinta matsayin wata daban, duk abin da ya je ya zo kuwa ita ta jaho. Dan wannan kowaye ya ji ya san dole a samu matsala a gaba, kuma abin da macen ke tsoro za ta iya janyo shi da kanta. Idan ma zargi take kan yana aikata wani abun, sai ta barshi shi da ubangijinsa ya fi mata.
Sunana Hauwa Abubakar Sarki, daga Suleja Jihar Neja:
Kishi na iya sa mace ta aikata komai, duk yadda mace ta kai ga bin diddigin mijinta da sanya ido akan al’muransa, wai dan saboda kada ya ƙara aure yayyo mata kishiya wallahi aikin banza ne. Idan mijinki ya yi niyyar aikata abu musamman ƙara aure kuma bai yi niyyar gaya maki ba duk buncikenki ba za ki taɓa ganewa ba. Kiran da zan yi a gare su shi ne su bari, duk abin ki, baki isa ki hana namiji abun da yayi niyya ba. Musamman akan ƙarin aure, addu’a da miƙa al’amura zuwa ga Allah shi ne kaɗai mafita a gare mu. Sosai kuwa, illah ta farko shi ne, idan har ki ka kamasa da abin da ki ke zargin yana aikatawa babu abun da zai haifar maki sai tashin hankali. Shawarar da zan basu shi ne, idan har ba saɓon Allah yake da wanda yake neman ba mafi a’ala shi ne ki bi shi da fatan alkhairi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp