Aminiya:
2025-08-08@22:27:01 GMT

Obi ya ziyarci Bauchi, ya ba da tallafin N15m don inganta ilimi

Published: 8th, August 2025 GMT

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ziyarci Jihar Bauchi tare da ba da tallafin Naira miliyan 15 don tallafa wa harkar ilimi.

Obi, ya sauka a filin jirgin sama na Abubakar Tafawa Balewa da misalin ƙarfe 9:40 na safe.

Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe

Bayan saukarsa ya wuce Makarantar Kiwon Lafiya da Koyon Aikin Jinya da Ungozoma ta Malikiya da ke Bauchi.

A yayin ziyarar, Obi ya gana da ɗaliban makarantar, inda ya roƙe su da su dage wajen karatu domin aikin jinya da kula da lafiya yana da matuƙar muhimmanci wajen ci gaban ƙasa.

Ya ce: “A yau, nasarar kowace al’umma tana dogara ne da lafiyar mutane. Ba za a iya maganar lafiya ba tare da an ambaci masu aikin jinya da ungozoma ba.

“Ana hasashen cewa nan da shekarar 2030, za a fuskanci ƙarancin ma’aikatan jinya a duniya. Wannan ya sa aikinku ke da matuƙar muhimmanci.”

Daga nan sai ya ba da tallafin Naira miliyan 10 ga makarantar a madadin ɗaliban da ma’aikata.

Shugaban makarantar, Alhaji Aminu Mohammed Danmalikin Bauchi, ya gode masa bisa wannan tallafi da kuma irin karamcin da ya nuna.

Bayan nan, Obi ya ziyarci makarantar Islamiyya ta Intisharu Tahfizul Qur’an da ke unguwar Yelwa, inda ya gana da malamai da ɗalibai.

Shugaban makarantar, Mallam Adamu Suleiman Jibril, ya bayyana farin cikinsa da ganin Obi, inda ya bayyana hakan a matsayin ƙauna ce da damuwa wajen ci gaban ilimin addini da kuma na zamani.

Obi, ya jaddada cewa yana matuƙar muhimmanci a bai wa matasa ilimi mai nagarta da tarbiyya.

“Mun zo yau saboda muna ganin muhimmancin sauraron muryar matasa da tunaninsu game da batutuwan da suka shafi rayuwarsu da ƙasar nan,” in ji shi.

Haka kuma, Obi ya kai ziyara Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU), inda ya tattauna da ɗalibai a kan batutuwan siyasa, tattalin arziƙi da ci gaban ƙasa.

A yayin wannan ziyarar, Obi yana tare da tsohuwar Ministar Kuɗi kuma muƙaddashiyar shugabar jam’iyyar LP na ƙasa, Nenadi Usman, da kuma jagoran ƙungiyar Obi, Salisu Ibrahim.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: makarantu ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore

Ana zargin wasu ‘yan sanda daga Sashen Binciken ‘yan sanda na Kasa sun kutsa inda ake tsare dan gwagwarmaya Omoyele Sowore a Abuja, inda suka fita da shi da karfin tuwo zuwa wani wuri da har yanzu ba a sani ba.   Haka kuma kamar yadda Sowore ya sanar a shafinsa na sada zumunta na Facebook, ya yi zargin cewa an karya hannunsa yayin da jam’an suka finciko shi da karfin tsiya daga inda yake tsare wajen qarfe 6:00 na safiyar yau Alhamis a kokarinsu na kai shi kotu ba tare da sanar da lauyansa ba..   A jiya Laraba ne dai Sowore ya amsa gayyatar da ofishin Babban Sufeton ‘Yan sanda na kasa ya yi masa don ya amsa wasu tambayoyi da suke da alaka da zanga-zangar da tsofaffin ‘yan sanda suka yi a makon jiya   Ana kuma son karin bayani kan zargin da Sowore ya yi na cewa, Babban Sufeton na Kasa ya kara wa jami’an ‘yan sandar da ke aiki a gidansa girma ba bisa ka’ida ba.   Sai dai ya yi watsi da zarge-zargen inda ya bayyana su a matsayin borin kunya da hukumar ‘yan sandan take don “dauke hankalin jama’a daga abin kunyar da Babban Sufeton na kasa Kayode Egbetokun da kuma hukumar ‘yan sandan ke aikatawa.   Tuni dai Kungiyar kare Hakkin Bil’Adama ta Amnesty International ta fitar da sanarwar yin Allah wadai da kamun da hukumar ‘yan sandan ta Najeriya ta yi wa Sowore wanda ta ce ya sba wa ‘yancinsa na fadin albakacin baki.   Haka kuma Amnesty International ta bukaci a saki Omoleye Sowore nan take ba tare da gindaya masa wasu sharuda ba.   Shi ma dan gwagwarmaya Bello Galadanci da aka fi sani da Dan Bello, ya yi tir da kamun da aka yi wa Sawore tare da kiran a sake shin an take kamar yadda ya rubuta a shafinsa na Facebook.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
  • An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi
  • Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore
  • Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
  • Ana zargin ‘yan sandan da karya hannun Sawore
  • Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi
  • Tinubu Ya Umurci A Bada Kulawar Lafiya Kyauta Ga Tsofaffin Ma’aikata Masu Karamin Fansho
  • Gwamnatin Kano Za Ta Farfado Da Makarantu Tare Da Kara Inganta Fannin Ilimi
  • Batun Ceto Wanda Ake Zargi Da Kwaya: Kwamishinan Kano Ya Yi Murabus