Aminiya:
2025-09-24@11:21:14 GMT

Obi ya ziyarci Bauchi, ya ba da tallafin N15m don inganta ilimi

Published: 8th, August 2025 GMT

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ziyarci Jihar Bauchi tare da ba da tallafin Naira miliyan 15 don tallafa wa harkar ilimi.

Obi, ya sauka a filin jirgin sama na Abubakar Tafawa Balewa da misalin ƙarfe 9:40 na safe.

Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe

Bayan saukarsa ya wuce Makarantar Kiwon Lafiya da Koyon Aikin Jinya da Ungozoma ta Malikiya da ke Bauchi.

A yayin ziyarar, Obi ya gana da ɗaliban makarantar, inda ya roƙe su da su dage wajen karatu domin aikin jinya da kula da lafiya yana da matuƙar muhimmanci wajen ci gaban ƙasa.

Ya ce: “A yau, nasarar kowace al’umma tana dogara ne da lafiyar mutane. Ba za a iya maganar lafiya ba tare da an ambaci masu aikin jinya da ungozoma ba.

“Ana hasashen cewa nan da shekarar 2030, za a fuskanci ƙarancin ma’aikatan jinya a duniya. Wannan ya sa aikinku ke da matuƙar muhimmanci.”

Daga nan sai ya ba da tallafin Naira miliyan 10 ga makarantar a madadin ɗaliban da ma’aikata.

Shugaban makarantar, Alhaji Aminu Mohammed Danmalikin Bauchi, ya gode masa bisa wannan tallafi da kuma irin karamcin da ya nuna.

Bayan nan, Obi ya ziyarci makarantar Islamiyya ta Intisharu Tahfizul Qur’an da ke unguwar Yelwa, inda ya gana da malamai da ɗalibai.

Shugaban makarantar, Mallam Adamu Suleiman Jibril, ya bayyana farin cikinsa da ganin Obi, inda ya bayyana hakan a matsayin ƙauna ce da damuwa wajen ci gaban ilimin addini da kuma na zamani.

Obi, ya jaddada cewa yana matuƙar muhimmanci a bai wa matasa ilimi mai nagarta da tarbiyya.

“Mun zo yau saboda muna ganin muhimmancin sauraron muryar matasa da tunaninsu game da batutuwan da suka shafi rayuwarsu da ƙasar nan,” in ji shi.

Haka kuma, Obi ya kai ziyara Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU), inda ya tattauna da ɗalibai a kan batutuwan siyasa, tattalin arziƙi da ci gaban ƙasa.

A yayin wannan ziyarar, Obi yana tare da tsohuwar Ministar Kuɗi kuma muƙaddashiyar shugabar jam’iyyar LP na ƙasa, Nenadi Usman, da kuma jagoran ƙungiyar Obi, Salisu Ibrahim.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: makarantu ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Ballon d’Or: Wa zai lashe kyautar 2025?

Ana ci gaba da takaddama a duniyar kwallon kafa kan wa ya fi cancanta da lashe kyautar Ballon d’Or a matsayin gwarzon dan wasan duniya na  bana.

A ranar Litinin din na za a bayar da Kyautar Ballon d’Or ta shekarar 2025 a birnin Paris na kasar Fasansa, ga wanda alakalai suka zaba a matsayin Gwarzon Dan Wasan Kwallon Kafa na Duniya.

Ballon d’Or ce kyauta mafi girma ta shekara-shekara ga ’yan wasan kwalllon kafa saboda bajintar da ya nuna ga ƙungiyarsa da ƙasarsa.

Gasar ta bana ta kasance mafi zafi duba da yadda alkaluma ke nuna irin zakakurancin kowanne daga manyan ’yan wasan da ake hasashen za su iya lashe kambin.

An rufe sansanin NYSC da kasuwanni saboda rashin tsaro a Kwara Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina

Ga jerin manyan ’yan wasa biyar da aka fi ganin suna da damar lashe ta bana:

Ousmane Dembélé – (PSG, Faransa)

Ousmane Dembélé ne ke kan gaba a jerin masu fafatawa.

Dembele ya ta rawa gani wajen kai PSG ga nasarar lashe kofuna uku – gasar Ligue 1, Coupe de France da kuma kofin Zakarun Turai na farko a tarihin kulob ɗin.

Ya zura kwallaye 21 tare da taimaka wajen cin wasu shida, musamman a muhimman wasanni.

Wannan ne yasa ake kallonsa a matsayin babban ɗan fafatawa.

2. Lamine Yamal – (Barcelona, Sifaniya)

Matashin ɗan shekara 17 zuwa 18 ya yi abin mamaki a wannan kakar.

Yamal ya yi fice a gasar La Liga da kuma Copa del Rey inda ya zura kwallaye 18 tare da taimakawa wajen cin kwallaye da bayar da dama aka ci wasu 21.

Kwarewarsa da kwazo suka sa ake kallon shi tamkar fitacciyar tauraruwa ta gaba.

Sai dai kuma duk da haka, rashin nasara a Gasar Zakaraun Turai na iya rage masa ƙuri’u.

3. Raphinha – (Barcelona, Brazil)

Shi ma Raphinha yana daga cikin manyan ’yan wasan da suka yi fice a bana.

Ya zura kwallaye 34 tare da bayar da damaa ka zura wasu 22 a muhimman wasanni.

Barcelona ta yi nasara a gida, kuma gudummawarsa ta zama abin yabo.

Amma duk da haka, ya na iya fuskantar kalubale wajen daga irin bambanci tsakaninsa da sauran taurarin Barcelona.

4. Vitinha – (PSG, Portugal)

Vitinha na daga cikin ɗan tsaka-tsaki da aka yaba da rawar da ya taka a PSG.

Shi ke tsare tsakiya, yana rarraba kwallo da samar da daidaito tsakanin tsaro da hari.

Duk da cewa ba shi da yawan kwallaye ko taimako irin na ’yan wasan gaba, gudummawarsana da matuƙar muhimmanci.

Sai dai irin wannan rawar kan kananan wurare na iya zama mai ƙarancin tasiri ga masu kada ƙuri’a.

5. Mohamed Salah – (Liverpool, Masar)

Salah ya ci gaba da zama ginshiƙi a Liverpool inda ya taimaka musu su lashe Gasar Firimiyar Ingila da kwallaye da dama da kuma taimakon cin wasu. A matsayinsa na ɗan wasa da ya dade yana taka rawar gani, yana da daraja a idanun masu jefa kuri’a.

Amma rashin kai Liverpool mataki mai nisa a Champions League na iya rage darajarsa a wannan karon.

Abubuwan da ke iya tabbatar da nasara?

Masu shirya gasar sun ce abubuwan da ake la’akari da su wajen zabar Gwarzon Dan Wasan su ne: Hazikancinsa shi kadai, dabi’unsa da iya yanke hukunci da kuma gudummawa ga abokan wasansa dai saurnasu kamar haka:

Lashe manyan kofuna musamman Champions League. Nuna kwazo a manyan wasanni kamar na karshe ko na kusa da karshe. Yawan kwallaye da taimako na da tasiri ga masu jefa kuri’a. Nasarorin kasa-kasa ma na iya ƙara daraja. Salonsa da kuma iya wasa ba tare da keta ba, kamar yadda matashin Yamal ya zo da sabon salo, na iya tasiri. Yiwuwar ba-zata

A halin yanzu, ana kallon Ousmane Dembélé a matsayin babban wanda ke iya lashe wannan babbar kyauta, yayin da Lamine Yamal ke biye masa.

Raphinha, Vitinha da Mohamed Salah kuwa suna nan a sahun gaba suna jiran rarrabuwar ƙuri’u wanda hakan ke iya sa su kai bantensu.

Duk da haka, Ballon d’Or ya saba zuwa abubuwan ban mamaki; duk wani ɗan wasa mai tasiri — mai tsaron raga, mai tsaron gida, ko wani fitacce —na iya mamaye sahun gaba idan ya nuna bajinta a ƙarshen kakar. 

Kazalika kokarin dan wasa na karshe-karshe musamman a Champions League ko wasannin kasashe na iya sauya kuri’un.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarihi da rayuwar Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh (1943-2025)
  • Jagora: Iran Ba Za Ta Taba Yin Watsi Da Inganta Sinadarin Uranium Ba
  • An ƙona al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ribas, Fubara Ya Ziyarci Tinubu A Fadar Gwamnati A Abuja
  • Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau
  • Ballon d’Or: Wa zai lashe kyautar 2025?
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa