Waɗan nan sune suka keɓe makomar Nijeriya, kuma suka yi garkuwa da ita. Har ila yau, a cewar majalisar dattawa ta 9 da ta yi bincike na sayar da ƙaddarorin gwamnati, wanan ɓarnar dukiyar ƙasa ne a rana tsaka, kuma kamar yadda ɗaya daga cikinsu ya bayyana kafin ya koma cikinsu, ya ce: “PRIƁATIZATION” ba komai ba ce face “PIRATIZATION” — wato sata da rabon ganima ce a fili.

Waɗannan su ne masu kuɗi na yaki haram -yaki halas ,da suka ƙwace jam’iyyu, suka wawure zaɓuka, suka yi watsi da kowa sai nasu, suka kashe baitul-mali, kuma yanzu suna neman dawowa bisa kan Karagar Mulki da sunan dimokuraɗiyya. Wannan cutar dimokuraɗiyyar Nijeriya ce da ke ƙara bazuwa, kuma yaudara ne gadan-gadan da rana tsaka!

Ko wanne cikinsu yana da tabon keta doka. Waɗannan ‘yan wasan kwaikwayo ba ‘yan adawa ba ne ga juna, amma abokai ne wajen wawure dukiyar ƙasa da kuma durƙusar da ƙasa marasa kishin Nijeriya ko ‘yan Nijeriya, wanda suke kama da Judasu da ke neman a dawo da shi cikin sahun Manzanni.

“Izaa Zulzilatil Ardu Zilzaalahaa”

“Idan ƙasa ta girgiza da girgizarta ta ƙarshe…” (Suratul Zilzalah, Aya ta 1)

Amma tambaya biyu?:

Lokacin da waɗannan bayi, ‘yan cartel, masu siyar da Nijeriya , suke rike da gwamnati daga 1999 zuwa 2025:

Me suka yi alkawari ga ‘yan Nijeriya?

Me aka tono game da su bisa kundin tsarin mulkin 1999 da dokar sayar da kamfanonin gwamnati (Priɓatization Act), da rahotannin kwamitin majalisa, da ƙasidan el-rufai da bayanan jaridun gaskiya kamar Premium Times, Guardian, Daily Trust, ThisDay, Ɓanguard, Punch, Sahara Reporters da sauransu?

Alƙawura: (Sakamakon ƙarancin wuri, za a kawo kaɗan daga ciki)

Rashin inganci na kamfanonin gwamnati yasa za a sayar da su

Tsauri da wahalar tafiyar da su

Yawan ma’aikata

Rashin riƙon amana

Cin hanci da rashawa

Nauyi ga gwamnati

Rage kashe kuɗi

Samar da ayyukan yi

Shigo da jarin da ƙasashen waje

Gyaran tattalin arziki

Ci gaban ilimi da lafiya

Bunƙasa noma

Yaki da fatara

Samar da tsaro da walwala da dai sauransu…

Amma Abin Da Suka Aikata: Suna da hannu a:

Sayar da Niger Dock, sun kori ma’aikata 3,600

Sayar da Eleme Petrochemicals -Kafanin da ta saye ta tamayar da kuɗin ta har da riban jarin a cikin watani 14 kacal.

ALSCON – An gina ta akan kuɗi dalar amurka $3.2bn, aka sayar da ita akan dalar amurka $130m.

Sayar da Daily Times, NICON Insurance, Transcorp Hilton, da Ughelli Power

NEPA, NITEL, Nigeria Airways, Delta Steel, da sauran su

Cire tallafin man fetur.

Rashin biyan fansho da hakkokin ma’aikata.

Ka da mu manta da labarin akwatuna 53 a fili tashin jirgin saman a legas ( wato the 53 Suitcases Saga).

Da labarin dalar amurka $40m da aka fitar zuwa Amurka.

Takardun makaranta jamiá da shaidar ƙaryar ta Chicago State Uniɓersity.

Raba kan ‘yan Nijeriya da salon tsarin musulim – musulim ticket.

Zargin cin hanci na Grass-cutting a san sanin ‘yan gudun hijira.

Biyan fensho har ƙarshen rayuwa ga manyan sakatarorin gwamnatin taraya (PERM.SECs) da shugaban ma’aikata(Heads of Serɓice) daga asusun IPPIS ba tare da sun bada gudunmawa ba , da dai sauran su.

Rusa tattalin arziki ta karyar da darajan naira.

Ƙarancin abinci da ilimi

Durkusar da noma da kiwo da kuma tsarin noma da ya tsaya cik

Mayar da asibitocin wajen hanyar samun kuɗin shiga da taɓarɓarewan kiwon lafiya.

Rashin tsaro da garkuwa da jama’a da dai sauransu…

Kada mu manta da wanna ayoyin

“Faman ya’mal mithƙaala tharratin khayran yarah”- (Suratul Zilzalah, Aya ta 7)

“Wa man ya’mal mithƙaala tharratin sharran yarah “-(Suratul Zilzalah, Aya ta 8)

“Zaɓin da ke Gaban ‘Yan Nijeriya”

To ga su kamar haka, ‘yan Nijeriya na cewa:

PDP – Power to the People? To ku dawo da duk ƙadarorin da aka siyar ba bisa ƙa’ida ba kuma a siyar da ƙadarorin Dubai domin a kafa cibiyoyin masana’antu na matasa.

APC – Renewed Hope? Ku dawo da tallafin da aka cire, kuma a mayar da gidan Naira biliyan 21 zuwa Asibitin Ƙasa mai daraja ta ɗaya.

ADA – Justice for All? To ku dawo da duk kuɗaɗen da aka wawure daga sayar da ƙadarori da sauran madaƙala da ya faru a ƙarƙashin zamanin ku.

ADC – Arise & Shine? To ku jabaya kuba Nijeriya da ‘yan Nijeriya damar tashi, da haskakawa da cin nasara.

Tsakanin dukkan su dake cikin PDP, APC, ADA da ADC sun more rayuwa, sunyi komai mai yuwuwa a ƙarƙashin sama ta ɗaya, halartatce da haramtatce, ko ƙarya ne?

To kada mu manta da wanna aya -“Fabi ayyi aala’i Rabbikumaa tukazzibaan?”- (Surah Ar-Rahman: Ayoyi 13 da sauran ayoyi 30)

A Ƙarshe”

Bari mu rufe sharhin da waɗannan kalmomi masu ratsa zuciyar bil adama masu tsoron Ubangiji :

“Inna Allaha ‘ala kulli shai’in shaheed” – Lalle Allah shaida ne a kan komai. (Surah Al-Mujadilah: 6)

“Wallahu khabeerun bima ta’maloon” – Allah yana sane da duk abin da kuke yi. (Surah Al-Hujurat: 18)

“Wa makaroo wa makarallah, wallahu khayrul makireen” – (Surah Al-Imran: 54)

(Su sami malamai su yi masu cikanken bayanin wannan aya)

“Yawma’izinyasdurun naasu ashtaatan liyuraw a’maalahum” – A ranar nan, mutane za su rabu sassa daban-daban domin a nuna musu ayyukansu (munana da kyawawa). (Surah Al-Zalzalah: 6)

Hon. (Alh) Adamu Rabiu (Bakondare)

Ƙwararre a fannin Kula da Ayyuka da Tantance su (M&E) kan Manufofi, Kuɗi, Siyasa da Gudanar da Gwam

nati Mai Kyau, kuma mai fafutukar Ci Gaba Mai Ɗorewa. Ya rubuto daga Kaduna

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yan Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

A ranar Juma’ar da ta gabata ne, Trump ya sake mayar da Nijeriya matsayin kasa mai matukar damuwa, sannan ya yi gargadin cewa; “idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bayar da izinin kashe kiristoci, nan take Amurka za ta dakatar da duk wani taimako da take bai wa Nijeriya, sannan kuma mai yiwuwa ta shiga kasar, domin kakkabe ‘yan ta’addan Islama da ke aikata wadannan munanan ayyuka na ta’addanci.”

Kazalika, ya kuma umarci Ma’aikatar Yakin Amurka, da ta shirya domin daukar mataki.

Pete Hegseth, Sakataren Yakin Amurka, a ranar Asabar ya ce; Ma’aikatar Yaki na shirin daukar mataki.

Barazanar Trump dai, ta biyo bayan zargin da wani dan majalisar dokokin Amurka, Ted Cruz, ya yi a shafinsa na D, a ranar 7 ga watan Oktoba na cewa; an kashe kimanin kiristoci 50,000, tun daga shekarar 2009 tare da lalata makarantu 2,000 da rusa Coci-coci 18,000, wanda musulmi masu dauke da makamai suka dauki nauyin aikatawa. Sai dai Cruz, bai ambaci tushen bayanan nasa ba.

A martanin da ya mayar, Shugaba Bola Ahmed Tinubu, a ranar Asabar da ta gabata, ya yi watsi da zargin da Trump ya yi wa Nijeriya, yana mai dagewa kan cewa; kasar ta ci gaba da kasancewa a matsayin dimokuradiyya mai tushe da tsarin mulkin kasar ya ba da ‘yancin yin addini.

A cewarsa, Nijeriya ta tsaya tsayin daka a matsayin dimokuradiyyar da kundin tsarin mulki ya ba da ‘yancin walwala.

Ya ce, tun daga shekarar 2023, gwamnatinsa ta ci gaba da kasancewa tare da shugabannin Kiristoci da na Musulmi baki-daya, sannan kuma tana ci gaba da magance matsalolin tsaro da suka shafi ‘yan kasa a fadin addinai da yankuna daban-daban.

“Yancin addini da juriya, sun kasance ginshikin tushenmu, kuma za su ci gaba da kasancewa a haka, Nijeriya na adawa da zalincin addini, sannan kuma ko kadan ba ta karfafe shi ba.

“Nijeriya kasa ce da kundin tsarin mulkinta ya bayar da tabbacin kare ‘yan kasa a kowane addini.

Gwamnatinmu, ta kudiri aniyar yin aiki tare da gwamnatin Amurka da sauran kasashen duniya, domin zurfafa fahimta da hadin gwiwa, kan kare al’ummomin dukkanin addinai,” in ji Tinubu.

Ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya, a wata sanarwa da kakakinta, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ya fitar a ranar Asabar ya ce: “Gwamnatin Tarayyar Nijeriya, ta lura da kalaman da shugaban kasar Amurka Donald J. Trump, ya yi a baya-bayan nan, game da kashe-kashen kiristoci da ake yi a Nijeriya tare da yin kira da a ayyana kasar a matsayin “Kasar da za a mayar da hankali a kai.”

“Yayin da Nijeriya ta yaba da damuwar duniya game da ‘yancin Dan’adam da ’yancin addini, wadannan ikirari, ba su nuna halin da ake ciki a kasar ba, ‘yan Nijeriya na dukkanin addinai, sun dade suna rayuwa tare, suna yin aiki tare, sannan kuma suna yin ibada tare a cikin lumana.

“A karkashin jagorancin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, Nijeriya ta jajirce wajen yaki da ta’addanci, karfafa hadin kan addinai da kare rayuka da ‘yancin al’ummarta.

“Nijeriya za ta ci gaba da yin aiki tare da gwamnatin Amurka, don zurfafa fahimtar juna game da yanayin yankin da kuma kokarin da ake yi na zaman lafiya da tsaro.”

 

Su Ma Musulmin Ana Kashe Su- Yankin Middle Belt

Shugaban Kungiyar ‘Middle Belt’ (MBF), Dakta Bitrus Pogu, ya bayyana cewa; ‘yan ta’addan kasar nan ne suke kashe musulmai kamar yadda suke kashe Kiristoci.

Ya ce, barazanar da Amurka ta yi, kira ne kawai na farkar da gwamnatin Nijeriyar, domin murkushe ‘yan ta’adda.

Ya kara da cewa; “Amurka ba ta fitar da wata barazanar daukar matakin soji ba, illa kawai ta sanya Nijeriya a matsayin kasa wadda ya kamata a sanya wa ido.

“Hakan yana nufin sanya takunkumi, shiga tsakani don tabbatar da cewa; an tilasta wa gwamnati yin abin da ya dace, sannan kuma; idan har za a dauki wani mataki na soja, wato na fatattakar ‘yan tada kayar baya, ba za a zama kasa daya ba, kana kuma; hakan zai faru ne kawai idan kasarmu ta ki yin abin da ya kamata ta yi.

“Haka zalika, a koda-yaushe na sha fadin cewa; sojojinmu na kokari kwarai da gaske, amma akwai masu zagon kasa a cikin jami’an tsaron, kuma daga lokaci zuwa lokaci, an yi ta samun hakan kamar a zamanin marigayi Buhari.

“Ana kashe mutane daruruwa babu wanda ya damu, sannan babu wanda aka kama a tsakanin mutanen da suke kai wannan hari, wadannan mutane za su zo su kai hari, amma har sai an bai wa sojoji umarni kafin su yi wani abu a kai ana ji ana kallo.

“Don haka, batu na gaskiya akwai matsala, sannan abin takaici kuma shi ne, duk wadannan kungiyoyi masu tayar da kayar baya a Arewa, suna kashe Kiristoci ne da kuma Musulmai, kana kuma suna kiran kungiyarsu da ta jihadi, wadanda a zahiri ba Musulmai ba ne.

 

Kungiyar ACF Ta Musanta Zargin Kisan Kiristoci Kadai

Kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF), a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadin da ta gabata, ta hannun sakataren yada labaranta na kasa, Farfesa Tukur Muhammad-Baba, ta yi gargadi game da mamayar da kasashen waje ke yi wa wata kasa mai cin gashin kanta ta Amurka.

ACF ta kuma yi nuni da cewa, ‘yan ta’adda a kasar nan, na kashe ‘yan Nijeriya daga kowane irin addini.

“Tare da dimbin bayanan sirrin da aka tura ko’ina, ya kamata a ce, Amurka ta fi kowa sanin halin da ake ciki na kisan da ake yi.

“Kamar sauran ‘yan Nijeriya masu kishin kasa, mambobin kungiyar tuntuba ta Arewa, sun samu labari mai cike da takaici game da ayyana Nijeriya a matsayin kasar da Amurka ta sanya wa ido,” in ji shi.

“Tuni dai ‘yan Nijeriya na kowane bangare na fama da hare-haren da wasu bata gari da suka hada da ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga, ‘yan tada kayar baya da masu tsattsauran ra’ayin addini a yankin Arewa maso Gabas, Arewa ta Tsakiya, Arewa maso Yamma, Kudu maso Gabas da sauran sassan kasar nan.

Ya kara da cewa “Shekaru da dama, kungiyar ACF na sane da cewa; gwamnatocin Nijeriya da suka biyo baya, sun roki Amurka da ta taimaka musu ba tare da wata fa’ida ba.”

Ya ce, duk wani tallafi daga kasashen waje ya kamata ya mayar da hankali wajen taimakawa sojojin Nijeriya, maimakon kai hari kan wata kungiyar addini.

Haka zalika, ACF ta gargadi ‘yan Nijeriya da su tuna da darussan tarihi, inda ta ambaci tsoma bakin da aka yi a Bietnam, Afghanistan, Syria, Irak da kuma kusa da gida, akwai Libya da Sudan, da kasashen Sahelian, har sai sun sake tunani, don lissafta wasu kadan.

Taron ya yi maraba da martanin da gwamnatin tarayya ta bayar, inda ta bayyana cewa; ya cancanci goyon bayan duk wanda abin ya shafa.

ACF ta kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su yi tunani mai zurfi game da lamarin tare da marawa gwamnati baya, yayin da take mayar da martani kan lamarin, sannan ta yi kira ga hadin kan yankin daga “Afirka da sauran kasashe.”

A cewar sanarwar: “Bisa la’akari da babban tasiri ga aikin Nijeriya, ACF za ta ci gaba da sa ido, tantancewa da kuma mayar da martani ga ci gaban al’amarin.”

Har ila yau, shugabannin addinai daban-daban a fadin wadannan kasa tare kuma da wasu jiga-jigai a fannin siyasa da sarakuna, sun yi watsi da wannan zargi na Kasar Amurka tare da barazanar da suka yi na kawo wa Nijeriya hari.

Baya ga watsi da wannan barazana da Trump ya yi, Rabaran John Joseph Hayab, ya yi kira ga Kiristoci da Musulmi daga Arewacin Nijeriya da su gudanar da tarukan hadin kai da zaman lafiya.

Rabaran Hayab, wanda shi ne Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN), na Jihohin Arewa 19 da kuma Babban Birnin Tarayya (FCT), ya ci gaba da ba da shawarar a rika tattaunawa tsakanin addinai, domin magance matsalolin da yankin ke fuskanta, kamar rashin tsaro da kuma rashin yarda da juna.

Haka nan, malaman addinin musulinci, kamar irin su Sheikh Ahamad Gumi, Sheikh Ibrahim Makari, Sarkin musulmi da sauran ‘yan siyasa kamar irin su Sanata Rabi’u Kwankwaso, Sanata Shehu Sani da Manjo Hamza Almustapha, sun yi kakkausan martani a kan wannan barazana da Kasar Amurka ta yi.

A ranar Talatar da ta gabata ne, Kasar Sin; ita ma ta shiga jerin cikin wadanda suka yi watsi da barazanar da Amurkan ta yi, na daukar matakin soji kan Nijeriya, tana mai cewa; tana matukar adawa da duk wani katsalanda daga waje a cikin harkokin cikin gidan kasar.

Matsayin gwamnatin kasar ta Sin, ya zo ne a ranar da gwamnatin tarayya ta ce; masu tsattsauran ra’ayin addini ne ke bayan wannan labari na zargin kisan kiyashi da ake yi wa Kiristoci, tare da cewa; babban burinsu shi ne, raba kan al’umma.

Ita ma a nata bangaren, Majalisar Dinkin Duniya; ta yi kira ga kasashe da su guji amfani da karfi, dangane da barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa Nijeriya, kan zargin kisan kiyashi da aka ce ana yi wa Kiristoci.

Har ila yau, a cikin jawabai daban-daban, Kungiyar Tarayyar Turai (EU) da Kungiyar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), sun yi gargadi kan ayyukan da za su iya yi wa Nijeriya zagon kasa, inda suka dage cewa; ta’addanci a yankin ya shafi dukkanin mabiya addinan guda biyu.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari  November 7, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT November 6, 2025 Manyan Labarai Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya  November 6, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu!
  • An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140