Kudirin gyaran dokar  fansho da sauran fa’idodi na tsaffin jami’an gwamnati ya wuce karatu na biyu a zauren Majalisar Dokokin Jihar Jigawa.

Wakilin mazabar Malam Madori, Alhaji Hamza Adamu Ibrahim wanda shi ne shugaban Kwamatin kasafin kudi na majalisar, shi ne ya gabatar da wannan kudurin, ya kuma samu goyon bayan wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari.

Alhaji Hamza Adamu Ibrahim ya yi bayanin cewar, daga cikin shugabanin da suka rike mukaman siyasa da ya kamata su amfana da irin wannan fansho sun hada da Gwamna da Mataimakan Gwamna da Shugaban Majalisar Dokoki da Kuma alfarmar da ya kamata su ci gaba da samu bayan sun bar mulki.

Bayan Akawun majalisar, Barrister Musa Aliyu Abubakar, ya gudanar da karatu na 2 akan kudurin sai Shugaban Majalisar Dokokin jihar Jigawa, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya kafa Kwamati na musamman mai Wakilai 7 da za su zagaya wasu daga cikin jihohin kasar nan domin gano yadda dokar ta ke aiki a wadancan jihohi.

Shugaban Masu Rinjaye na majalisar Kuma wakilin mazabar Roni, Alhaji Lawan Muhammad Dansure shi ne shugaban Kwamatin, yayin da wakilin mazabar Malam Madori Alhaji Hamza Adamu Ibrahim da na mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari da mazabar Fagam Alhaji Yahaya Zakari Kwarko da na mazabar Taura, Alhaji Dayyabu Shehu da na mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da na mazabar Bulangu Alhaji Yusuf Ahmad Soja su ka kasance wakilan kwamatin.

An bai wa Kwamatin mako 4 domin ya gudanar da wannan aiki sannan ya mika rahoton sa ga zauren majalisar dokokin jihar jigawan.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa da na mazabar

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Ruman Katsina ya rasu

A yau Litinin Allah Ya yi wa Sarkin Ruman Katsina kuma Hakimin Batsari, Alhaji Tukur Ma’azu, rasuwa.

Marigayin, wanda ya shafe shekaru 74 a duniya, ya daɗe yana fama da jinya gabanin rasuwarsa.

Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja

Alhaji Tukur wanda ya shafe shekaru 43 yana riƙe da sarautar Hakimin Batsari, ya rasu ya bar mata biyu, ’ya’ya da kuma jikoki.

Za a gudanar da jana’izarsa da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin yau a gidansa da ke cikin garin Batsari, kamar yadda sanarwa daga iyalansa ta tabbatar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa
  • Majalisar Dattawa Ta Buɗe Ofishin Sanata Natasha
  • An yi garkuwa da ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Dalilin da muke goyon bayan tsare-tsaren Tinubu na karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Sarkin Ruman Katsina ya rasu
  • Bayan Mutuwar Wani Matashi, An Kafa Dokar Ta Baci A Yauri
  • Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka
  • Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya
  • Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York