Kudirin gyaran dokar  fansho da sauran fa’idodi na tsaffin jami’an gwamnati ya wuce karatu na biyu a zauren Majalisar Dokokin Jihar Jigawa.

Wakilin mazabar Malam Madori, Alhaji Hamza Adamu Ibrahim wanda shi ne shugaban Kwamatin kasafin kudi na majalisar, shi ne ya gabatar da wannan kudurin, ya kuma samu goyon bayan wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari.

Alhaji Hamza Adamu Ibrahim ya yi bayanin cewar, daga cikin shugabanin da suka rike mukaman siyasa da ya kamata su amfana da irin wannan fansho sun hada da Gwamna da Mataimakan Gwamna da Shugaban Majalisar Dokoki da Kuma alfarmar da ya kamata su ci gaba da samu bayan sun bar mulki.

Bayan Akawun majalisar, Barrister Musa Aliyu Abubakar, ya gudanar da karatu na 2 akan kudurin sai Shugaban Majalisar Dokokin jihar Jigawa, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya kafa Kwamati na musamman mai Wakilai 7 da za su zagaya wasu daga cikin jihohin kasar nan domin gano yadda dokar ta ke aiki a wadancan jihohi.

Shugaban Masu Rinjaye na majalisar Kuma wakilin mazabar Roni, Alhaji Lawan Muhammad Dansure shi ne shugaban Kwamatin, yayin da wakilin mazabar Malam Madori Alhaji Hamza Adamu Ibrahim da na mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari da mazabar Fagam Alhaji Yahaya Zakari Kwarko da na mazabar Taura, Alhaji Dayyabu Shehu da na mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da na mazabar Bulangu Alhaji Yusuf Ahmad Soja su ka kasance wakilan kwamatin.

An bai wa Kwamatin mako 4 domin ya gudanar da wannan aiki sannan ya mika rahoton sa ga zauren majalisar dokokin jihar jigawan.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa da na mazabar

এছাড়াও পড়ুন:

Zan ci gaba da siyasa har ƙarshen rayuwata – Shekarau

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, ya ce zai ci gaba da yin siyasa matuƙar yana numfashi a doron duniya.

Shekarau ya bayyana cewar siyasa wata babbar hanya ce ta hidima wa jama’a.

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Don Yaki da Laifuffuka A Maiduguri Abba ya yaba wa sojoji kan hallaka ’yan bindiga 19 a Kano

Yayin da yake hira da ’yan jarida a Kano a yayin bikin zagayowar ranar haihuwarsa na cika shekaru 70, Shekarau, inda ya ce gina siyasarsa ne bisa tafarkin addini da ɗabi’a.

“Siyasata addinina ce, addinina kuma siyasata ce. Shiga cikin tsarin samar da shugabanni na gari masu gaskiya hidima ce ga jama’a kuma wannan ibada ce a Musulunci,” in ji shi.

Tsohon gwamnan ya bayyana cewa, siyasarsa ba ta da nasaba da son kai, sai dai niyyar ganin an samar da shugabanni masu adalci da kishin al’umma.

“Matukar ina da ƙarfi, zan ci gaba da bayar da gudunmawa. A gare ni siyasa ba aiki ba ne da ake daina yi; nauyi ne na rayuwa gaba ɗaya,” in ji shi.

Shekarau, wanda ya mulki Jihar Kano daga 2003 zuwa 2011, ya yi kira ga jam’iyyun adawa da su haɗa kai domin ƙarfafa dimokuraɗiyya.

Ya kuma yi kira ga shugabanni su mayar da hankali kan matsalolin rashin tsaro, talauci da yunwa.

Ya kuma yaba wa jam’iyyar PDP bisa juriyarta inda ya bayyana cewar har yanzu tana taka muhimmiyar rawa a siyasar Najeriya.

Ya kuma yi wa makomar siyasar Najeriya fatan alheri, tare da jadadda cewa zai ci gaba da goyon bayan kowace gwamnati don samar da zaman lafiya da jin daɗin ’yan ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah
  • Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu
  • Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu
  • Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai
  • Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 
  • Zan ci gaba da siyasa har ƙarshen rayuwata – Shekarau