Majalisar Jigawa Ta Yi Karatu Na Biyu Kan Dokar Fansho Ga Tsofaffin Shugabanni
Published: 8th, August 2025 GMT
Kudirin gyaran dokar fansho da sauran fa’idodi na tsaffin jami’an gwamnati ya wuce karatu na biyu a zauren Majalisar Dokokin Jihar Jigawa.
Wakilin mazabar Malam Madori, Alhaji Hamza Adamu Ibrahim wanda shi ne shugaban Kwamatin kasafin kudi na majalisar, shi ne ya gabatar da wannan kudurin, ya kuma samu goyon bayan wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari.
Alhaji Hamza Adamu Ibrahim ya yi bayanin cewar, daga cikin shugabanin da suka rike mukaman siyasa da ya kamata su amfana da irin wannan fansho sun hada da Gwamna da Mataimakan Gwamna da Shugaban Majalisar Dokoki da Kuma alfarmar da ya kamata su ci gaba da samu bayan sun bar mulki.
Bayan Akawun majalisar, Barrister Musa Aliyu Abubakar, ya gudanar da karatu na 2 akan kudurin sai Shugaban Majalisar Dokokin jihar Jigawa, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya kafa Kwamati na musamman mai Wakilai 7 da za su zagaya wasu daga cikin jihohin kasar nan domin gano yadda dokar ta ke aiki a wadancan jihohi.
Shugaban Masu Rinjaye na majalisar Kuma wakilin mazabar Roni, Alhaji Lawan Muhammad Dansure shi ne shugaban Kwamatin, yayin da wakilin mazabar Malam Madori Alhaji Hamza Adamu Ibrahim da na mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari da mazabar Fagam Alhaji Yahaya Zakari Kwarko da na mazabar Taura, Alhaji Dayyabu Shehu da na mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da na mazabar Bulangu Alhaji Yusuf Ahmad Soja su ka kasance wakilan kwamatin.
An bai wa Kwamatin mako 4 domin ya gudanar da wannan aiki sannan ya mika rahoton sa ga zauren majalisar dokokin jihar jigawan.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa da na mazabar
এছাড়াও পড়ুন:
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya
Hukumar Kula da Dokokin Hanya ta Jihar Legas (LASTMA) ta rufe wani gidan casu mai suna Vaniti Club House da ke kan titin Adeola Odeku a Victoria Island bisa laifin karya dokar harkokin sufuri ta shekarar 2018.
A cewar LASTMA, an rufe gidan casun ne saboda ajiye motoci ba bisa ƙa’ida ba a gefen titi da kuma toshe hanyoyi, lamarin da ke haddasa cunkoso da barazana ga lafiyar jama’a. Wannan matakin ya samu jagorancin babban daraktan hukumar, Olalekan Bakare-Oki, tare da sashen ceto da tabbatar da doka.
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos Kwalara Ta Kashe Mutane 5 A Lagos, An Kai 60 Asibiti Ranga-RangaHukumar ta ce wannan mataki na ɗaya daga cikin tsarin sabbin dabarun sa ido da aiwatar da doka a faɗin Legas, kuma gwamnatin jihar na da ƙudurin tabbatar da tsari, da tsaro, da ingantaccen tsarin zirga-zirga.
Shugaban LASTMA ya gargaɗi cibiyoyin nishaɗi, kamfanoni da jama’a da kada su yi katsalandan ga zirga-zirgar ababen hawa ko su haifar da haɗari ga lafiyar al’umma. Ya kuma buƙaci mazauna Legas su riƙa kai rahoto idan akwai cibiyar taro da ke hana zirga-zirga ta layukan gaggawa na LASTMA.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp