Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Published: 9th, August 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Ban ɓata zargin Shettima da ƙirƙiro Boko Haram ba — Sheriff
Tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa ya taɓa zargin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da ƙirƙiro Boko Haram.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Sanata Sheriff ya bayyana labarin a matsayin ƙarya mara tushe.
Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar NajeriyaYa ce bai taɓa yin wata hira ko yi wa wani bayani da ya shafi Shettima game da kafa Boko Haram ba.
“Wannan labari ƙarya ne gaba ɗaya, kuma an shirya shi ne domin rikita jama’a da kawo rabuwar kai,” in ji sanarwar.
Sheriff, wanda tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, ya ce waɗanda suka yaɗa wannan labari suna ƙoƙarin rage ƙimarsa da kuma ɓata gudunmawar da yake bayarwa wajen samar da zaman lafiya da haɗin kai a Jihar Borno da Najeriya baki ɗaya.
Ya ce ya umarci lauyoyinsa su gano waɗanda suka yaɗa labarin tare da ɗaukar matakin shari’a a kansu.
“Idan ba a gaggauta goge wannan labari daga kafafen da suka yaɗa shi ba, zan ɗauki matakin shari’a,” in ji Sheriff.
Sanata Sheriff, ya roƙi ’yan Najeriya da kafafen watsa labarai da su yi watsi da labarin, tare da bin gaskiya da adalci wajen yaɗa bayanansu.