Majalisar Kano Ta Karbi Kudirin Karamin Kasafin Kudi Na Shekarar 2025
Published: 12th, August 2025 GMT
Majalisar dokokin jihar Kano ta karbi karin kudirin kasafin kudi na shekarar 2025 daga bangaren zartarwa na jihar domin tantancewa.
Bukatar, wacce aka mika ta wata wasika daga bangaren zartarwa, ta nemi amincewar majalisar ta kara kasafin kudi naira biliyan 169,522,463,294.82 domin daukar muhimman ayyukan raya kasa a fadin jihar.
Kakakin majalisar Alhaji Jibril Isma’il Falgore ya bayyana cewa hukumar zartaswa na kokarin ganin an kara wa kasafin kudin domin gudanar da ayyuka masu ma’ana da za su shafi rayuwar mazauna.
Bayan sun yi duba, ‘yan majalisar sun mika kudirin dokar ga kwamitin kasafin kudi na majalisar domin tantancewa da daukar matakin da ya dace.
A wani labarin kuma, Majalisar ta kuma samu takarda daga bangaren zartarwa na tantance Barista Saidu Yahaya a matsayin sabon shugaban hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano (PCACC).
Nadin ya biyo bayan cikar wa’adin tsohon shugaban Barista Muhyi Magaji Rimin Gado.
An mika sunan ga kwamitin majalisar kan korafin jama’a don ci gaba da aiwatar da doka.
Majalisar ta dage zaman ta ne zuwa washegari sakamakon kudirin da shugaban masu rinjaye, Lawan Hussaini Dala ya gabatar.
COV/Khadija Aliyu08164127760
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad
Ta ce, “Dole ne akwai kalubale da dama, wanda daga cikinmu muke fuskanta a yayin shigowa wannan masana’anta, amma dai ni babu wani abu da zan iya tunawa, illa wani wanda na iske a masana’antar ya karbi zunzurutun kudi har Naira 50,000 a mabanbantan lokuta da sunan zai yi min rijista a masana’antar, kuma bai yi ba, daga karshe ma na gano cewa; kudin rijistar duka-duka Naira 5,000 ne.
A wata hira da Khadija ta yi da gidan Rediyon Hikima, ta bayyana cewa, matukar ta samu abin da ya kawo ta masana’antar (Kudi), to nan da shekara daya ma; za ta iya shiga daga ciki, ma’ana za ta samu miji ta yi aurenta na Sunna.
Khadija, wadda ta ce; ita haifaffiyar birnin Maiduguri ce ta Jihar Borno, wadda zama ya dawo da ita birnin Kanon Dabo, ta kuma bukaci masu kallon su da su dinga nuna musu soyayya kamar yadda suke nuna wa sauran jaruman duniya, musamman wadanda ke cikin masana’antar Bollywood ta Kasar Indiya.
“Akwai bukatar dukkaninmu, mu hada karfi da karfe don ganin mun taimaki junanmu, ba mu koma gefe muna zagin junanmu ba, abin da ya sa na fadi haka kuwa shi ne, akwai lokacin da wani ya zo neman aurena, amma wasu suka zagaya baya suka hure masa kunne a kan cewa; kada ya sake ya aure ni, saboda ni jarumar fim ce. Ta kara da cewa; mu ma Hausawa ne kamar mafi yawan masu kallonmu, sannan kuma bai kamata ku yi la’akari da duk wani abu da kuka gani a cikin fim, wajen yanke hukuncin cewa, halin dan fim kenan ko a zahiri ba.
Daga karshe, Khdadija ta ce; “Dukkanninmu ‘yan fim, muna kokari wajen ganin mun killace kanmu( Sirrinta al’amuranmu), domin kauce wa zargi, duk wani wanda ka ga yana fallasa halayensa na zahiri a shafukansa na sada zumunta, to ba dan fim ba ne, kawai yana zuwa neman taimako wajen masu shirya fina-finai ne su saka shi ya fito sau biyu ko sau uku a fim, domin su samu na cefane, amma ba lallai ne ya zama cikakaken dan fim ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA