Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano
Published: 8th, August 2025 GMT
Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Wakilai, Abubakar Kabir Abubakar, ya ce Gwamnatin Tarayya za ta kashe Naira tiriliyan daya da rabi don gina layin dogo na zamani domin saukaka harkar sufuri a cikin birnin Kano.
Ya bayyana hakan ne lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a Kano, inda ya ce aikin zai saukaka wa mazauna birnin wahalar da suke sha a harkar sufuri.
Ya ce, “Wannan aikin na gina layin dogo na zamani ya kai Dalar Amurka biliyan daya, kwatankwacin Naira tiriliyan daya da rabi.
“Ga wadanda suke tafiye-tafiye zuwa kasashen waje, musamman kasashen Turai da nahiyar Asiya, sun san akwai irin wadannan ayyukan kuma suna da muhimmanci. Aikin zai kara habaka tattalin arzikin jihar idan aka kammala shi.”
Dan majalisar ya kuma ce sabanin yadda ake yadawa, Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya bullo da muhimman ayyukan raya kasa a bangarorin lafiya da aikin gona da ilimi da kuma tsaro a Arewacin Najeriya.
“Abin mamaki ne idan na ji wasu mutane na cewa Shugaba Tinubu bai damu da Arewa ba. Ni ne shugaban kwamitin kasafin kudi, kuma na san me ya yi wa Arewa.
“Ya kamata mu ajiye son rai a gefe guda mu fada wa kanmu gaskiya a kan Shugaba Tinubu. Ya bijiro da ayyuka da dama a Arewa da ya kamata a yaba masa,” in ji Abubakar Bichi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: layin dogo
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamishinan ‘Yan Sanda Na Jihar Kano Ya Sha Alwashin Kawar Da Badala A Harkokin Fina-finai
Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cikakken goyon bayan rundunar ‘yan sanda ga Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano wajen tabbatar da kiyaye dabi’u da yakar munanan halaye a cikin al’umma.
CP Bakori ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar wayar da kai da Sakatare na Hukumar, Abba El-Mustapha, ya kai tare da tawagarsa zuwa hedikwatar rundunar ‘yan sandan Kano.
A yayin ganawar, CP Bakori ya yaba da jagorancin hukumar, musamman kokarin da El-Mustapha ke yi wajen tsara harkokin masana’antar Kannywood da kuma kare tarbiyya ta hanyar sa ido mai tsauri.
Ya tabbatar da ci gaba da hadin gwiwa tsakanin rundunar da hukumar, musamman wajen dakile cin zarafi da amfani da kafafen sada zumunta wajen yada munanan abubuwa da kuma kare mutuncin jama’a.
“Rundunar ‘yan sanda a Kano za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da hukumar domin tabbatar da doka da oda da kuma kare tarbiyya a kananan hukumomi 44 na jihar.” In ji CP Bakori.
A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Tace Fina-finai, Abba El-Mustapha, ya taya CP Bakori murna bisa sabon nadin da aka masa, tare da jaddada bukatar hadin gwiwa mai karfi tsakanin ‘yan sanda da hukumar.
Ya ce tsaftace fina-finai da sauran abubuwan da ke shafar kafafen watsa labarai ba zai yiwu ba sai da goyon bayan hukumomin tsaro.
“Muna daraja hadin gwiwarmu da rundunar ‘yan sanda, wanda hakan ya taimaka mana wajen tabbatar da bin ka’ida da kare dabi’u a jihar Kano.” In ji El-Mustapha.
Ya kuma gode wa kwamishinan bisa kyakkyawar tarba da kuma jajircewarsa wajen goyon bayan aikin hukumar, yana mai jaddada kudirin hukumar na ci gaba da sa ido a kafafen watsa labarai da fina-finai, daidai da al’adu da dabi’un al’ummar Kano.
Khadijah Aliyu