Alkaluman kididdiga na hukumar kwastam ta kasar Sin sun nuna yadda cikin watanni 7 na farkon shekarar nan ta 2025, jimillar darajar cinikayyar kayayyaki ta kasar Sin ta kai kudin kasar yuan tiriliyan 25.7, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 3.5, wanda hakan ya nuna karuwar kashi 3.5 cikin 100 idan aka kwatanta da makamancin lokaci na shekarar bara.

Daga cikin adadin, darajar mizanin fitar da kayayyaki ya kai yuan tiriliyan 15.31, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 2.1, adadin da ya karu da kashi 7.3 cikin 100, yayin da mizanin shigo da kayayyaki shi ma ya kai yuan tiriliyan 10.39, kwatankwacin dalar Amurka triliya 1.44, adadin da ya ragu da kashi 1.6 cikin 100.

 

A watan Yuli, jimillar darajar cinikayyar kayayyaki ta Sin ta kai yuan tiriliyan 3.91 kwatankwacin dalar Amurka biliyan 544, adadin da ya karu da kashi 6.7 cikin 100. Daga wannan adadi, mizanin fitar da kayayyaki ya kai yuan tiriliyan 2.31, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 321, inda ya karu da kashi 8 cikin 100. Sai kuma mizanin shigo da kayayyaki da ya kai darajar yuan tiriliyan 1.6, kwatankwacin dala biliyan 222, wanda shi ma ya karu da kashi 4.8 cikin 100, wanda hakan ke nuna ci gaba da karuwarsa a tsawon watanni biyu. (Amina Xu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kwatankwacin dalar Amurka kai yuan tiriliyan ya karu da kashi da kayayyaki

এছাড়াও পড়ুন:

An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai

Al’ummar Ƙauyen Sarai da ke Ƙaramar hukumar Dawakin Kudu a Jihar Kano sun shiga ruɗani a ranar Alhamis bayan da aka gano gawar wata mata mai shekara 96 ​​a cikin  masai.

Jami’in hulɗa da jama’a na Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya bayyanawa manema labarai a ranar Juma’a.

Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800

Abdullahi ya ce, sashin bayar da agajin gaggawa na hukumar ya samu kiran gaggawa daga wani mai suna Usman Adamu ranar Alhamis, inda ya bayyana cewa wata tsohuwa ta faɗa cikin masai a ƙauyen Sarai.

“Hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Daraktan, Sani Anas ta samu kiran gaggawa daga Usman Adamu da misalin ƙarfe 9:27 na safiyar ranar Alhamis, 6 ga watan Nuwamba, 2025, inda ya bayar da rahoton ibtila’in da wata mata ta faɗa cikin ramin masai a ƙauyen Sarai da ke ƙaramar hukumar Dawakin Kudu,” a cikin sanarwar.

“Jami’anmu na sashen agajin gaggawa daga hedikwatar hukumar ta isa wurin, inda ta gano wata mata mai suna Habiba Ado mai shekara 96, wanda ’yan uwanta suka ce tana fama da taɓin hankali,” in ji shi.

Abdullahi ya bayyana cewa, ‘yan uwanta ​​sun shafe kwanaki huɗu suna nemanta kafin a gano gawarta a cikin masai ranar Alhamis.

“Sun kuma yi kira ga mai gidan da ya rufe ramin masan don hana afkuwar irin haka nan gaba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa jami’an ceto sun gano  matar daga cikin ramin, amma an tabbatar da mutuwar ta.

Tuni dai aka miƙa gawarta ga Hakimin Unguwa, Alhaji Musa Muhammad domin yi mata jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai
  • Yaduwar Juyin Mulki A Afirka
  • Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya
  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka