An Rantsar Da Sabbin Mataimaka Na Musamman A Karamar Hukumar Auyo
Published: 9th, August 2025 GMT
An shawarci sabbin mataimaka na musamman da su kasance masu adalci da gaskiya wajen aiwatar da ayyukansu a ƙaramar hukumar Auyo ta jihar Jigawa.
Shugaban ƙaramar hukumar Auyo, Alhaji Binyaminu Ahmad Adamu Kafur ne ya bayar da wannan shawara yayin bikin rantsar da sabbin mataimaka na musamman 69 da aka gudanar a Auyo.
Alhaji Binyaminu Kafur ya sake tabbatar da kudirin majalisar wajen yin aiki tare da masu ruwa da tsaki domin samar da kayayyaki more rayuwa, don tabbatar da ganin kowa ya amfana da mulkin dimokuraɗiyya.
Ya yi kira ga jama’a da kada su gaji wajen yin addu’a domin samun nasarar shugabanni wajen aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su inganta rayuwarsu.
Shi ma a nasa jawabin, Alhaji Umar Jura ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar bisa zabar mutanen da suka dace don yin aiki a lokacin mulkinsa.
Ya yi kira ga waɗanda aka naɗa da su bada haɗin kai tare da yin aiki tukuru don nuna amincewar da aka nuna gare su.
A madadin waɗanda aka naɗa, Malam Yakubu Muhammad Auyo da tsohon shugaban rikon ƙwarya Mika’ila Auyo sun gode wa shugaban ƙaramar hukumar bisa amincewa da su don yin wannan aiki.
Haka kuma sha alwashin haɗin kai domin cimma manufofin da aka sanya a gaba.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa ƙaramar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
UNGA: Yau Shettima zai gabatar da jawabin Najeriya a MDD
Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima a ranar Laraba zai gabatar da jawabin Najeriya a taron Babban Zauren Majalisar Dinkin duniya (UNGA) karo na 80 da ke gudana a birnin New York na Amurka.
Zai yi jawabin ne a madadin Shugaban Kasa Bola Tinubu tsakanin karfe 3:00 na yamma zuwa 9:00 na dare agogon birnin New York.
Mun ci ribar Naira biliyan 601 a watanni shidan farkon 2025 – Bankin GT Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar WakilaiKamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa ana sa ran Najeriya za ta bayyana sabbin kudurorinta na kasa (NDCs) da aka sabunta a karkashin yarjejeniyar Paris yayin wannan jawabi.
A baya, Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya halarci zaman bude taron Majalisar Dinkin Duniya, inda Shugaban Amurka, Donald Trump, ya gabatar da jawabi na musamman, yana maraba da shugabannin duniya zuwa taron.
Da yake magana da NAN kan muhimmancin jawabin na Najeriya Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai da Sadarwa (Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), Stanley Nkwocha, ya ce ana sa ran sakon Najeriya ya karade duniya.
“Ko a fannin diflomasiyyar ilimi, al’adu, wasanni, tsaro, ko diflomasiyyar tattalin arziki, Shugaba Tinubu ya sauya yadda Najeriya ke mu’amala da al’ummar duniya.
“Ya gyara salon manufofin kasashen waje na Najeriya.
“Idan kana son auna karfin muryar Najeriya a matakin duniya, ka tuna da jawabin da ya gabatar a UNGA na shekarar 2024.
“Jawabi ne mai karfi da ya bukaci a yi sauye-sauye, ciki har da karin kujeru ga kasashen Afrika a Kwamitin Tsaro na MDD,” in ji Nkwocha.
(NAN)