An Rantsar Da Sabbin Mataimaka Na Musamman A Karamar Hukumar Auyo
Published: 9th, August 2025 GMT
An shawarci sabbin mataimaka na musamman da su kasance masu adalci da gaskiya wajen aiwatar da ayyukansu a ƙaramar hukumar Auyo ta jihar Jigawa.
Shugaban ƙaramar hukumar Auyo, Alhaji Binyaminu Ahmad Adamu Kafur ne ya bayar da wannan shawara yayin bikin rantsar da sabbin mataimaka na musamman 69 da aka gudanar a Auyo.
Alhaji Binyaminu Kafur ya sake tabbatar da kudirin majalisar wajen yin aiki tare da masu ruwa da tsaki domin samar da kayayyaki more rayuwa, don tabbatar da ganin kowa ya amfana da mulkin dimokuraɗiyya.
Ya yi kira ga jama’a da kada su gaji wajen yin addu’a domin samun nasarar shugabanni wajen aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su inganta rayuwarsu.
Shi ma a nasa jawabin, Alhaji Umar Jura ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar bisa zabar mutanen da suka dace don yin aiki a lokacin mulkinsa.
Ya yi kira ga waɗanda aka naɗa da su bada haɗin kai tare da yin aiki tukuru don nuna amincewar da aka nuna gare su.
A madadin waɗanda aka naɗa, Malam Yakubu Muhammad Auyo da tsohon shugaban rikon ƙwarya Mika’ila Auyo sun gode wa shugaban ƙaramar hukumar bisa amincewa da su don yin wannan aiki.
Haka kuma sha alwashin haɗin kai domin cimma manufofin da aka sanya a gaba.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa ƙaramar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC?
Wannan irin jita-jitar tana kokain zana shi da kwatankwacin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp