Aminiya:
2025-11-10@04:11:14 GMT

Al-Hilal ta ɗauki Nunez daga Liverpool

Published: 10th, August 2025 GMT

Kungiyar Al Hilal ta Saudiyya ta dauki dan wasan gaban Liverpool, Darwin Nunez, kamar yadda kungiyoyin biyu suka tabbatar ranar Asabar.

Masu ruwa da tsaki a harkar tamaula na ganin wannan matakin za bai wa zakarun Premier League damar sake mika tayin neman dan wasan gaban Newcastle, Alexander Isak.

ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram a Borno

Shekaru uku da suka gabata ne Nunez ya koma Liverpool daga Benfica kan farashin Yuro miliyan 75 ($87m, £65m), sai dai bai iya cika tsammanin da aka yi wa darajar da aka saye shi ba.

Nunez wanda dan kasar Uruguay ne ya zura kwallaye 40 a wasanni 143 da ya haska a Liverpool, amma daga baya ya daina samun damar buga wasanni sosai a karkashin jagorancin Jurgen Klopp da Arne Slot.

Kafafen yada labarai na Birtaniya sun ruwaito cewa a karon farko Al-Hilal za ta biya Yuro miliyan 53 na farashin dan wasan mai shekara 26.

Bayanai sun ce ko da ba a cefanar da dan wasan ba, ba zai samu damar buga wasanni a wannan kakar ba, la’akari da cewa Liverpool ta dauki Hugo Ekitike da Florian Wirtz wanda ta kashe Yuro miliyan 300 ciki har da ’yan baya da ta saya da suka hada da Milos Kerkez da Jeremie Frimpong.

Sayar da Nunez ya kara yawan kudaden da Liverpool ta samu wajen cefanar da ’yan wasa a wannan kakar zuwa kusan Yuro ,iliyan 200 bayan tafiyar Luis Diaz, Jarell Quansah, Caoimhin Kelleher, Trent Alexander-Arnold da Tyler Morton.

Nunez shi ne sabon tauraron da ya koma Al-Hilal — kungiyar da ta bai wa Manchester City mamakin doke ta wasan kwata-final na gasar Club World Cup da aka gudanar a watan jiya.

Al-Hilal, karkashin jagorancin tsohon kocin Inter Milan Simone Inzaghi, na da ’yan wasan Portugal Ruben Neves da Joao Cancelo, kyaftin din Senegal Kalidou Koulibaly, da kuma tsohon dan wasan gaba na Fulham Aleksandar Mitrovic.

AFP

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

“Lamarin daya kai miliyan daya na wadanda suka nemi a basu bashin karatu, lalle abin ya nuna a gaskiya matasa sun son su kyautata yadda rayuwarsu data wasu zata kasance a gaba, musamman ma yadda suka maida hankali wajen neman ilimi.

Ya ci gaba da bayanin “Wannan yana nunawa a fili yadda jagorancin na Shugaban kasa Bola Tinubu ya damu da lamarin ilimi domin shi ne ginshikin ci gaban al’umma kamar yadda ya ce,”.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ilimi Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu October 18, 2025 Ilimi Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma October 18, 2025 Ilimi Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU October 18, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL
  • NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
  • Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
  • Dan Wasan Taekwando Na Kasar Iran Abulfazl Zandi Ya Zamo Shi Ne Na Daya A Duniya
  • Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata
  • NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho