Aminiya:
2025-08-08@19:33:43 GMT

’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe

Published: 8th, August 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta kama wasu matasa biyu da ake zargi da damfarar mutane a wajen cirar kuɗi a ATM.

Kakakin rundunar, SP Dungus Abdulkareem, ya ce an kama Umar Abubakar mai shekara 24 da Abdulaziz Mohammad mai shekara 25 daga Ƙaramar Hukumar Kumbotso, a Jihar Kano.

PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027 Isra’ila za ta mamaye ilahirin Zirin Gaza ya koma karkashinta – Netanyahu

An kama su lokacin da suke ƙoƙarin yaudarar wani mutum a wajen ATM na bankin Fidelity da ke Damaturu.

Ana zargin matasan da amfani da wasu dabara wajen damfarar mutane ta hanyar nuna kamar suna taimaka musu, amma daga baya sai su sauya musu katin ATM.

A wani labari kuma, jami’an ’yan sanda a Potiskum sun kama Usman Suleman mai shekara 25 daga Ƙaramar Hukumar Babura, a Jihar Jigawa, bisa zargin satar Keke Napep.

An kama shi lokacin da mai mai babur ɗin ya je sallah a masallaci da ke kusa da bankin Access a garin Potiskum.

An kama shi a Jihar Bauchi yayin da yake ƙoƙarin kai Keke Napep ɗin zuwa Jihar Kano.

A halin yanzu, ana ci gaba da bincike kan waɗanda ake zargin kafin gurfanar da su a gaban kotu.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado, ya jinjina wa jami’ansa bisa ƙwazon da suka nuna.

Ya kuma gargaɗi masu aikata laifi da su daina, inda ya tabbatar da cewa Jihar Yobe ba za ta zama mafaka ga masu aikata laifi ba.

Ya buƙaci al’umma da su ci gaba da kai rahoton duk wani abu da ya shige masu duhu zuwa ofishin ’yan sanda mafi kusa da su.

Ya kuma gode wa al’umma bisa haɗin kai da taimako da suke bai wa rundunar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Damfara zargi

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

Dabbobi 199 da aka sace (shanu 161 da tumaki 68) Motoci guda 3 da aka sace Babura 2 da ake zargi an sace su Miyagun ƙwayoyi da yawa ciki har da tabar wiwi Wayoyin wutar lantarki da aka lalata

DSP Aliyu ya yaba wa gwamnatin Jihar Katsina da al’ummar jihar saboda haɗin kai da suka bayar, yana mai cewa ba za a cimma nasarorin ba tare da taimakon jama’a ba.

Ya buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa ‘yansanda goyon baya, tare da kai rahoton duk wani abun zargi ta waɗannan layukan gaggawa: 0815697777722, 0902220969033, da 07072722539.

“Rundunar ‘Yansandan Jihar Katsina za ta ci gaba da ƙoƙarinta don kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina
  • Jami’ar Bayero Ta Bayyana Alhininta Bisa Kisan Gillar Wani Dalibinta
  • ’Yan sanda sun ƙwato jariri da aka sace a asibitin Ekiti
  • An kama bama-baman da aka boye a cikin kayan gwangwan a Kaduna
  • Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore
  • Ana zargin ‘yan sandan da karya hannun Sawore
  • Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
  • Jami’an Alhazai Sun Karrama DG Labbo Bisa Nasarar Hajjin 2025
  • Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma