’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe
Published: 8th, August 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta kama wasu matasa biyu da ake zargi da damfarar mutane a wajen cirar kuɗi a ATM.
Kakakin rundunar, SP Dungus Abdulkareem, ya ce an kama Umar Abubakar mai shekara 24 da Abdulaziz Mohammad mai shekara 25 daga Ƙaramar Hukumar Kumbotso, a Jihar Kano.
PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027 Isra’ila za ta mamaye ilahirin Zirin Gaza ya koma karkashinta – NetanyahuAn kama su lokacin da suke ƙoƙarin yaudarar wani mutum a wajen ATM na bankin Fidelity da ke Damaturu.
Ana zargin matasan da amfani da wasu dabara wajen damfarar mutane ta hanyar nuna kamar suna taimaka musu, amma daga baya sai su sauya musu katin ATM.
A wani labari kuma, jami’an ’yan sanda a Potiskum sun kama Usman Suleman mai shekara 25 daga Ƙaramar Hukumar Babura, a Jihar Jigawa, bisa zargin satar Keke Napep.
An kama shi lokacin da mai mai babur ɗin ya je sallah a masallaci da ke kusa da bankin Access a garin Potiskum.
An kama shi a Jihar Bauchi yayin da yake ƙoƙarin kai Keke Napep ɗin zuwa Jihar Kano.
A halin yanzu, ana ci gaba da bincike kan waɗanda ake zargin kafin gurfanar da su a gaban kotu.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado, ya jinjina wa jami’ansa bisa ƙwazon da suka nuna.
Ya kuma gargaɗi masu aikata laifi da su daina, inda ya tabbatar da cewa Jihar Yobe ba za ta zama mafaka ga masu aikata laifi ba.
Ya buƙaci al’umma da su ci gaba da kai rahoton duk wani abu da ya shige masu duhu zuwa ofishin ’yan sanda mafi kusa da su.
Ya kuma gode wa al’umma bisa haɗin kai da taimako da suke bai wa rundunar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Damfara zargi
এছাড়াও পড়ুন:
An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
Ana zargin wata matar aure, Rabi Nuhu da ke garin Magama Gumau a ƙaramar hukumar Toro ta Jihar Bauchi, da cin zarafin wata yarinya ’yar shekara biyar ta hanyar ƙone mata al’aura, saboda zargin tana yawan yin fitsarin kwance.
Wakilinmu ya gano cewa yarinyar marainiya ce wadda mahaifiyarta ta rasu kusan shekara ɗaya da ta gabata, inda take zaune tare da mahaifinta, Mohammed Umar, da matarsa.
CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100 Mahara sun kashe ɗan sanda sun ɗauke bindigarsa a TarabaWani mai fafutukar kare haƙƙin bil’adama a garin, Kabiru Abdulkadir, ya bayyana cewa sai bayan kwana biyar da ƙonewar ta faru ne al’amarin ya bayyana.
“Don guje wa matsala, mahaifin yarinyar ya sayi wata katifa ta daban domin ta riƙa kwanciya a kai, amma duk da haka matar tasa ba ta daina azabtar da yarinyar ba,” in ji Kabiru.
Aminiya ta ruwaito cewa, lamarin ya bayyana ne lokacin da yarinyar ta roƙi kawunta ya saya mata katifa, inda ta shaida masa cewa mamanta ta ƙona al’aurarta saboda yawan fitsarin kwance, dalili ke nan da ya yi wa ’yan sanda ƙorafi.
Kazalika, ana zargin cewa duk lokacin da matar ta samu sabani da mijinta, sai ta huce fushi a kan yarinyar.
Da yake jawabi, mahaifin yarinyar, Mohammed Umar, wanda ke aiki da wani gidan talabijin, ya tabbatar da cewa matarsa ta kan yi ƙorafi kan yawan fitsarin kwancen yarinyar, abin da ya sa ya saya mata katifa ta daban.
Umar ya ce: “A farko, da na ga ƙuna a jikinta, matata ta shaida min wai shayi mai zafi ne ya zubo a jikinta. A lokacin na gaskata hakan, har sai da na lura da ciwon yana ƙaruwa.”
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, CSP Mohammed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa rahoto ya iso ofishin su da misalin ƙarfe 3:00 na ranar 13 ga Satumba, 2025.
Wakil ya ce yarinyar ta sami ƙonuwa a ƙasan cikinta, cinyoyinta, da kuma al’aurarta.
Ya ƙara da cewa, kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Sani Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a gaggauta kama matar tare da miƙa ta zuwa sashen manyan laifuka domin gudanar da cikakken bincike.
Ya bayyana cewa da zarar an kammala binciken, za a gurfanar da ita a gaban kotu.