Araqchi ya mika rubutaccen sakon Jagora ga Shugaba Putin na Rasha
Published: 18th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya mika rubutacciyar wasikar jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ga shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.
Araghchi, wanda ya je birnin Moscow a matsayin shugaban tawagar diflomasiyya don ganawa da wasu manyan jami’an Rasha, ya gana da Putin a yammacin ranar Alhamis.
Ministan ya gabatar da sakon Jagoran ga shugaban kasar Rasha tare da bayyana ra’ayoyi da matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran dangane da batutuwan da suka shafi ajandar huldar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yanki da sauran batutuwa na kasa da kasa.
Araghchi ya tabo yarjejjeniyar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare da shugaba Putin da takwaransa na Iran, Masoud Pezeshkian suka rattabawa hannu a birnin Moscow a watan Janairu.
Ya kira wannan yarjejeniya a matsayin “aiki mafi mahimmanci ta fuskar hadin gwiwa” tsakanin kasashen biyu, yana mai jaddada aniyar Iran na karfafawa da fadada huldar dake tsakaninta da tarayyar Rasha a dukkan matakai.
Shugaba Putin ya isar da gaisuwa da fatan alheri ga Jagoran juyin juya halin Musulunci tare da jaddada muhimmancin kara karafa kawance tsakanin Iran da Rasha bisa manyan tsare-tsare.
Ya kara da cewa, karfafa alaka a tsakanin kasashen biyu, tare da hadin gwiwa kan batutuwan da suka shafi gabas ta tsakiya da na kasa da kasa, zai yi amfani da moriyar kasashen biyu, da taimakawa wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Baya ga hakan kuma sun duba sauran batutuwa da suka shafi yakin Ukraine da kuma tattauna batun shawarwari kan nukiliyar Iran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m a hanyar Jos
Sojoji sun kama wani ƙasurgumin mai garkuwa da mutane ɗauke da tsabar kuɗi Naira miliyan 13 a kan hanyar Kaduna zuwa Jos a Jihar Kaduna.
Dakarun Rundunar Operation Safe Haven sun kuma ƙwace bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da harsasai 30 a hannun ɗan ta’addan a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna.
Kakakin rundunar, Manjo Samson Zhakom, ya ce dubun ɗan ta’addan ta cika ne a wani shingen bincike da ke yankin Agameti a kan babbar hanyar Wamba zuwa Jos.
Manjo Zhakom ya ce a ranar Laraba, sojoji suka tsayar da wata mota ƙirar Volkswagen Golf da ke ɗauke da mutum uku, amma kafin ta ƙaraso inda za ta tsaya, biyu daga cikin mutanen suka fice suka tsere.
Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu MusawaYa bayyana cewa sojojin sun gano ramin harbin bindiga da kuma jini a jikin motar, kuma direban ya yi yunƙurin ba su cin hanci amma suka ƙi karba.
“Suka kama shi, bayan cikar wanda ake zargin da kuma cikin motar suka gano bindigogi biyu ƙirar AK-47 da harsasai 30 da wayoyi guda uku da layu da tsabar kuɗi N13,742,000, da wuƙa da sauransu.
“A yayin bincike ya amsa cewa yana da hannu garkuwa da mutane a kan hanyar Jos zuwa Makurɗi, kuma ya amince ya kai sojoji maɓoyarsa.
“A yayin da suke tafiya, wanda ake zargin ya yi yunƙurin ƙwace makamin jami’anmu, amma suka murƙushe shi” in ji shi.
Manjo Zangon ya ce rundunar na ci gaba da zurfafa bincike domin kamo sauran ’yan ta’addan da kuma tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.