Araqchi ya mika rubutaccen sakon Jagora ga Shugaba Putin na Rasha
Published: 18th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya mika rubutacciyar wasikar jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ga shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.
Araghchi, wanda ya je birnin Moscow a matsayin shugaban tawagar diflomasiyya don ganawa da wasu manyan jami’an Rasha, ya gana da Putin a yammacin ranar Alhamis.
Ministan ya gabatar da sakon Jagoran ga shugaban kasar Rasha tare da bayyana ra’ayoyi da matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran dangane da batutuwan da suka shafi ajandar huldar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yanki da sauran batutuwa na kasa da kasa.
Araghchi ya tabo yarjejjeniyar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare da shugaba Putin da takwaransa na Iran, Masoud Pezeshkian suka rattabawa hannu a birnin Moscow a watan Janairu.
Ya kira wannan yarjejeniya a matsayin “aiki mafi mahimmanci ta fuskar hadin gwiwa” tsakanin kasashen biyu, yana mai jaddada aniyar Iran na karfafawa da fadada huldar dake tsakaninta da tarayyar Rasha a dukkan matakai.
Shugaba Putin ya isar da gaisuwa da fatan alheri ga Jagoran juyin juya halin Musulunci tare da jaddada muhimmancin kara karafa kawance tsakanin Iran da Rasha bisa manyan tsare-tsare.
Ya kara da cewa, karfafa alaka a tsakanin kasashen biyu, tare da hadin gwiwa kan batutuwan da suka shafi gabas ta tsakiya da na kasa da kasa, zai yi amfani da moriyar kasashen biyu, da taimakawa wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Baya ga hakan kuma sun duba sauran batutuwa da suka shafi yakin Ukraine da kuma tattauna batun shawarwari kan nukiliyar Iran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
Tsarin yanayin masana’antu na Masar yana bunkasa kan fitar da kayayyaki zuwa Turai da Gabas ta Tsakiya. Tare da kasancewa mai karfi a cikin sinadarai, siminti, da kantin magani, Masar ta sanya kanta a matsayin jagorar masana’antun nahiyar da ke goyan bayan gyare-gyaren masana’antu.
An san kasar da samar da siminti, yadudduka, magunguna, da sinadarin man fetur da sauransu.
Sai kuma kasar Nijeriya mai rike da kambu na uku wacce ta kasance mai samun habaka a bangaren kasuwanci da masana’antu. Kamfanonin Dangote, musamman matatarsa da kuma rukunin kamfanonin BUA sun taimaka wa kasar wajen jan ragamar a bangaren masana’antu.
Manyan masana’antun kasar nan sun hada da na siminti, kayayyakin mabukata, abinci da abin sha, da tace mai, wanda manyan masana’antun kamar Dangote Group, BUA Group, Nestlé Nigeria, da Unileber Nigeria ke gudanarwa.
Morocco kuwa babbar cibiyar masana’antu ce a Arewacin Afirka, tana jawo hannun jari kai tsaye daga ketare a manyan masana’antu kamar kera motoci da hada-hadar jiragen sama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp