HausaTv:
2025-12-04@06:44:43 GMT

Araqchi ya mika rubutaccen sakon Jagora ga Shugaba Putin na Rasha

Published: 18th, April 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya mika rubutacciyar wasikar jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ga shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.

Araghchi, wanda ya je birnin Moscow a matsayin shugaban tawagar diflomasiyya don ganawa da wasu manyan jami’an Rasha, ya gana da Putin a yammacin ranar Alhamis.

Ministan ya gabatar da sakon Jagoran ga shugaban kasar Rasha tare da bayyana ra’ayoyi da matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran dangane da batutuwan da suka shafi ajandar huldar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yanki da sauran batutuwa na kasa da kasa.

Araghchi ya tabo yarjejjeniyar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare da shugaba Putin da takwaransa na Iran, Masoud Pezeshkian suka rattabawa hannu a birnin Moscow a watan Janairu.

Ya kira wannan yarjejeniya a matsayin “aiki mafi mahimmanci ta fuskar hadin gwiwa” tsakanin kasashen biyu, yana mai jaddada aniyar Iran na karfafawa da fadada huldar dake tsakaninta da tarayyar Rasha a dukkan matakai.

Shugaba Putin ya isar da gaisuwa da fatan alheri ga Jagoran juyin juya halin Musulunci tare da jaddada muhimmancin kara karafa  kawance tsakanin Iran da Rasha bisa manyan tsare-tsare.

Ya kara da cewa, karfafa alaka a tsakanin kasashen biyu, tare da hadin gwiwa kan batutuwan da suka shafi gabas ta tsakiya da na kasa da kasa, zai yi amfani da moriyar kasashen biyu, da taimakawa wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Baya ga hakan kuma sun duba sauran batutuwa da suka shafi yakin Ukraine da kuma tattauna batun shawarwari kan nukiliyar Iran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya: Matatar Man Fetur ta Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba

Matatar Man Fetur ta Dangote a Najeriya ta sanar a wannan  Litinin cewa tana da ikon isar da lita biliyan 1.5 na man fetur a kowane wata, kuma ta yi kira ga hukumar kula da masana’antu da ta tabbatar da hakan a cikin alkalumanta na yau da kullun, bayan da hukumar ta fitar da bayanai da ke nuna cewa matatar tana samar da kusan kashi daya bisa uku ne kawai na wannan adadi.

Ikirarin da ake yi cewa matatun man fetur na Najeriya ba su iya biyan bukatun kasa ba wani bangare ne na dalilin da ya sa gwamnati ta yi watsi da shirinta na hana shigo da kayayyakin man fetur da aka tace a watan da ya gabata ba.

Matatar ta kiyasta bukatar da ake da ita a Najeriya da cewa ya kai kusan lita miliyan 55 a kowace rana, wato kimanin lita biliyan 1.67 a kowane wata.

Matatar Dangote ta ce a shirye take ta samar da wannan adadi, kuma za ta iya yin hakan, inda a yanzu za ta iya samar da lita biliyan 1.5 na man fetur a kowane wata daga wanann watan Disamba da Janairu, inda kuma za ta kara adadin zuwa lita biliyan 1.7 a kowane wata daga watan Fabrairun 2026 zuwa gaba.

Matatar ta kuma bukaci Hukumar Kula da Man Fetur da Iskar Gas ta Jihar New Mexico (NOG) da ta tallafa wa ayyukanta ta hanyar barin shigo da danyen mai, da sauran kayayyakin da take bukata ba tare da wani cikas ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20 December 2, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165 December 1, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164 December 1, 2025 Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya December 1, 2025 Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3  A Kasar Lebanon December 1, 2025 Kamaru: Madugun Adawa Ya Rasu A Gidan Kaso December 1, 2025 Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi December 1, 2025 Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100% December 1, 2025 Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta December 1, 2025 Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagora: Musulunci Ya Daukaka Mata Matukar Dauka
  • Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci
  • Shugaba Pizishkiyan:  Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufar
  • An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Janar Christopher Musa Sabon Ministan Tsaro
  • Ministan Tsaron Najeriya  Ya Mika Takardar Ajiye Aiki Ga Shugaban Kasa Ahmad Tinubu.
  • Iran Bata Taba yin Watsi Da Diplomasiya Ba Amurka Ce Ke Kai Mutane Bango
  • Najeriya: Matatar Man Fetur ta Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba