Araqchi ya mika rubutaccen sakon Jagora ga Shugaba Putin na Rasha
Published: 18th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya mika rubutacciyar wasikar jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ga shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.
Araghchi, wanda ya je birnin Moscow a matsayin shugaban tawagar diflomasiyya don ganawa da wasu manyan jami’an Rasha, ya gana da Putin a yammacin ranar Alhamis.
Ministan ya gabatar da sakon Jagoran ga shugaban kasar Rasha tare da bayyana ra’ayoyi da matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran dangane da batutuwan da suka shafi ajandar huldar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yanki da sauran batutuwa na kasa da kasa.
Araghchi ya tabo yarjejjeniyar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare da shugaba Putin da takwaransa na Iran, Masoud Pezeshkian suka rattabawa hannu a birnin Moscow a watan Janairu.
Ya kira wannan yarjejeniya a matsayin “aiki mafi mahimmanci ta fuskar hadin gwiwa” tsakanin kasashen biyu, yana mai jaddada aniyar Iran na karfafawa da fadada huldar dake tsakaninta da tarayyar Rasha a dukkan matakai.
Shugaba Putin ya isar da gaisuwa da fatan alheri ga Jagoran juyin juya halin Musulunci tare da jaddada muhimmancin kara karafa kawance tsakanin Iran da Rasha bisa manyan tsare-tsare.
Ya kara da cewa, karfafa alaka a tsakanin kasashen biyu, tare da hadin gwiwa kan batutuwan da suka shafi gabas ta tsakiya da na kasa da kasa, zai yi amfani da moriyar kasashen biyu, da taimakawa wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Baya ga hakan kuma sun duba sauran batutuwa da suka shafi yakin Ukraine da kuma tattauna batun shawarwari kan nukiliyar Iran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun
Babban Sufeton ’yan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya ce sun janye ’yan sanda 11,566 da ke rakiyar manyan mutane kamar yadda Shugaban Ƙasa ya ba da umarni a kwanakin baya.
Ya kuma ce an sake tura waɗannan jami’an zuwa muhimman wuraren da aka fi buƙatars su don kare al’ummomi masu rauni a fadin ƙasa.
NAJERIYA A YAU:Waiwaye Kan Irin Gudunmawar Da Sheikh Dahiru Bauci Ya Bayar Ga Cigaban Addini An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a AnambraAminiya ta rawaito cewa Shugaba Bola Tinubu, a ranar Lahadi, ya bayar da umarnin janye jami’an ‘yan sanda daga aikin tsaron manyan mutane tare da umartar a sake tura su zuwa ayyukan tsaro na asali.
Umarnin ya biyo bayan taron tsaro da aka gudanar a Abuja tare da shugabannin rundunonin tsaro da shugaban hukumar tsaro ta DSS.
Yayin da yake jawabi a hedikwatar ’yan sanda da ke Abuja, ranar Alhamis, lokacin da ya gana da manyan jami’an ‘yan sanda masu mukamin kwamishina, Egbetokun ya ce jami’an da aka janye za a mayar da su ga ayyukan tsaro na asali.
Ya ce shawarar janye jami’an daga aikin tsaron mutanen ba ta samo asali daga son rai ba, sai dai daga bukatar gaggawa ta karkatar da ma’aikata zuwa wuraren da tsaron jama’a ya fi bukata.
A cewarsa, wannan mataki ya yi daidai da babban aikin Hukumar ‘Yan Sanda ta Najeriya, wato kare ‘yan ƙasa, al’ummomi da kuma tabbatar da zaman lafiya, yana mai jaddada cewa dukkan jami’an 11,566 da aka janye an sake tura su wuraren aiki.
“A bisa umarnin Shugaban Ƙasa, mun janye jami’an 11,566 daga aikin tsaron manyan mutane. Waɗannan jami’an za a sake tura su zuwa muhimman ayyukan tsaro nan take,” in ji shi.
Babban Sufeton ya ce janyewar za ta bai wa ‘yan sanda damar ƙara yawan jami’an da za su yi aiki wajen tsaron ƙauyuka da birane, kare jama’a da yawa, ƙarfafa sintiri, ayyukan tsaro bisa bayanan sirri, da kuma daƙile barazanar tsaro cikin gaggawa.