Aminiya:
2025-08-10@15:48:21 GMT

’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato

Published: 10th, August 2025 GMT

An sake shiga tashin hankali a Jihar Sakkwato bayan wani sabon mummunan hari da ’yan bindiga suka kai a wasu kauyuka, lamarin da ke ƙara tsananta matsalar tsaro a faɗin jihar.

Rahotanni sun nuna cewa duk shekara musamman a lokacin damina, ’yan bindiga sukan ƙara ƙaimi wajen kai hare-haren da ke tarwatsa jama’a a garuruwansu da hana manoma zuwa gona ko kuma ƙaƙaba musu harajin zuwa gonakin.

An ɗaure tsohon Firaminista Succes Masra shekaru 20 a Chadi Dan wasan Barcelona Inigo Martinez ya koma Al-Nassr

Aminiya ta ruwaito cewa, a bana ma, maharan sun ci gaba da addabar mazauna ƙananan hukumomi 20 daga cikin 23 na Jihar Sakkwato.

Majiyoyi sun tabbatar cewa a harin baya-bayan nan, ’yan ta’addan sun hallaka mutane da dama sannan sun yi garkuwa da wasu.

Shafin Bakatsine da ke bibiyar rahotannin da suka shafi sha’anin tsaro, a wannan Lahadin ya wallafa a manhajar X cewa, an kai hari a wani masallaci a garin Bushe da ke Karamar Hukumar Sabon Birni, inda aka sace aƙalla mutum 10 ciki har da limamin masallacin.

Rundunar ’yan sandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa ana ci gaba da ƙoƙarin ceto waɗanda aka sace.

Haka kuma, rahotanni sun ce maharan sun sake kai wani hari a lokacin sallar Isha a ƙauyen Marnona na Karamar Hukumar Wurno, a daren Asabar, inda suka kashe masallata da dama sannan suka yi awon gaba da wasu.

Sanata Ibrahim Lamido, mai wakiltar Sakkwato ta Gabas a Majalisar Dattawa, ya yi Allah wadai da hare-haren da suka auku a Bushe da Marnona, inda ya buƙaci hukumomi su ƙara ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyar al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana alhini kan rasuwar Sadiq Gentle, wani hadiminsa kan harkokin yada labarai a Ma’aikatar Tarihi da Al’adu ta jihar, wanda wasu da ake zargi ’yan daba suka kai masa harin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya wallafa a Facebook, ta bayyana Sadiq a matsayin jarumi, ƙwararre, kuma mai kishin kasa a fannin kafafen sada zumunta.

NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026 An kashe mutum huɗu da tayar da ƙauyuka 17 a Sakkwato

Gwamna Abba ya ce mutuwar Sadiq Gentle ta girgiza shi sosai, inda ya bayyana mamacin a matsayin mutum mai kamun kai, haƙuri, da sadaukarwa ga ci gaban Jihar Kano.

Gwamnan ya bayyana kisan da aka yi masa a matsayin keta haddin bil’adama da ba za a lamunta ba, lamarin da bayyana a matsayin ƙoƙarin da wasu bata-gari ke yi domin kawo cikas a zaman lafiya a jihar.

Ya umarci hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike, tare da tabbatar da cewa wadanda suka aikata wannan aika-aikar sun fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

Ya kuma jaddada cewa gwamnatin jihar ba za ta lamunci irin wannan ta’asa ba, yana mai bayyana bukatar tsauraran matakan tsaro domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kazalika, Gwamnan ya mika ta’aziyya ga iyalan marigayin, abokan aikinsa, da daukacin jami’an Ma’aikatan Tarihi da Al’adu, yana mai tabbatar musu da cewa Gwamnatin Kano na tare da su a wannan lokaci na jimami da baƙin ciki.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne wasu da ake zargi ’yan daba ne suka sassari hadimin gwamnan yayin wani farmaki da suka kai masa har gida da adduna.

Daga bisani an garzaya da Sadiq Gentle Asibitin Murtala da ke birnin Kano inda a nan ajali ya katse masa hanzari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi
  • Ana Alhinin Tunawa Da Harin Nukiliyar Nagasaki Shekarau 80 Da Suka Gabata A Japan
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
  • UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari
  • Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano
  • An kashe mutum huɗu da tayar da ƙauyuka 17 a Sakkwato
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara