Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Published: 9th, August 2025 GMT
A ranar Juma’a da yamma, wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun tare motar haya a mararrabar Ogbabo, kan titin Itobe-Anyigba a jihar Kogi, inda suka yi awon gaba da fasinjoji 9. Direban motar da wasu fasinjoji 6 kuwa sun tsere ba tare da an sace su ba.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:20 na yamma a yankin ƙaramar hukumar Ofu, lokacin da ƴan bindigar suka fito daga daji suka tare titin.
Nisan wurin da aka sace fasinjojin ya yi kusan mita 300 kacal daga shingen Sojoji na irin Ogbabo-Ochadamu. Jami’an tsaro sun isa wurin cikin gaggawa, inda suka tarar da motar haya mai lambar ENZ-55 XS da wata Toyota Carina ‘E’ a ajiye. An fara aikin ceto tare da haɗin gwuiwar ƴansanda, da Sojoji, da ƴan sa-kai da mafarauta domin gano masu laifin da kuma kuɓutar da waɗanda aka sace.
Kakakin rundunar ƴansanda jihar, SP Williams Ovye Aya, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran jami’an tsaro don ceto mutanen da aka sace tare da kama waɗanda suka aikata laifin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
“Lamarin daya kai miliyan daya na wadanda suka nemi a basu bashin karatu, lalle abin ya nuna a gaskiya matasa sun son su kyautata yadda rayuwarsu data wasu zata kasance a gaba, musamman ma yadda suka maida hankali wajen neman ilimi.
Ya ci gaba da bayanin “Wannan yana nunawa a fili yadda jagorancin na Shugaban kasa Bola Tinubu ya damu da lamarin ilimi domin shi ne ginshikin ci gaban al’umma kamar yadda ya ce,”.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA