UNICEF Da Gavi Sun Bada Na’urorin Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Ga Jihar Kano
Published: 11th, August 2025 GMT
Asusun Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) tare da haɗin gwiwar Gavi da ke taimakawa wajen samar da rigakafi, sun mika na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana g Gwamnatin Jihar Kano domin amfani da su a cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko (PHCs) guda 28 da nufin ƙarfafa rigakafin yara da kuma kula da lafiyar jama’a.
A yayin bikin mika kayayyakin ga gwamnatin jihar da Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Ƙasa (NPHCDA), Kwamishinan Lafiya na Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusuf, ya ce wannan shiri na nufin taimaka wa yaran da ba a musu rigakafi, da mata masu juna biyu da ba su da damar samun rigakafin yau da kullum da kuma wasu ayyukan kiwon lafiya.
“UNICEF tare da Gavi, ƙarƙashin shirin ƙarfafa tsarin kiwon lafiya na CDS3, sun tallafa wajen saka na’urorin hasken rana a cibiyoyin PHC na kananan hukumomin da ke da yawan yaran da ba a musu rigakafi a Najeriya.” In ji Dakta Labaran.
Ya ce Kano ce ta fi kowace jiha a Najeriya yawan yaran da ba a taba yi wa rigakafi ba, yana mai jaddada cewa cibiyoyin da aka saka musu wadannan na’urorin za su taka muhimmiyar rawa wajen kawar da matsalar.
Wannan aiki ya biyo bayan binciken yadda cibiyoyin lafiya a matakin farko ke aiki da wutar lantarki da UNICEF ta tallafa a shekarar 2023, wanda ya gano cibiyoyi 371 da suka cancanci a saka musu na’urorin. A wannan matakin, tare da haɗin gwiwar eHealth Systems Africa, an samar da wutar hasken rana a cibiyoyi 28 a Kano.
Tsarin zaɓen cibiyoyin ya mayar da hankali kan cibiyoyin kiwon lafiya a kananan hukumomin da ke da yawan yaran da ba a musu rigakafi, tare da cire waɗanda wasu ayyuka irin su CRIBS da IMPACT suka riga suka rufe, da kuma mayar da hankali kan cibiyoyin da ba su da ingantacciyar wutar lantarki.
Dakta Labaran ya gargadi jami’an da ke kula da cibiyoyin da kada su karkatar da su don amfani na kashin kansu.
Daraktan Ƙasa na Gavi, Jessica Crawford, ta bayyana cewa wannan karamcin wani ɓangare ne na ƙoƙarin haɗin gwiwa don ƙarfafa tsarin kiwon lafiya a Kano, inda ta ƙara da cewa Gavi za ta kashe kusan dala miliyan biyar a jihar cikin shekara biyu masu zuwa domin tallafawa manufofi da shirye-shiryen gwamnati wajen inganta lafiyar mata da yara.
Mai riƙon mukamin Shugaban Ofishin UNICEF a Kano, Michael Banda, wanda ya wakilci Shugaban Ofishin, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah, ya bayyana shirin a matsayin mataki na gina tsarin kiwon lafiya mai ɗorewa da adalci ga kowa.
Ya bayyana cewa samun wutar lantarki mai inganci na taimakawa wajen adana rigakafi yadda ya kamata, yin aiki a kowane lokaci, da rage dogaro da man fetur.
Taron ya samu halartar Darakta Janar na Hukumar Kula da Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Kano, Farfesa Salisu Ibrahim, da wakilai daga WHO, Gidauniyar Gates, da sauran abokan haɗin gwiwa.
Daga Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: wutar lantarki yaran da ba a kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
Kungiyar ‘Yan Dako ta kasa reshen jihar Jigawa ta kaddamar da Malam Muhammad Tajudeen Maigatari a matsayin sakataren kungiyar na jihar.
Da yake jawabin a lokacin bikin kaddamawar a garin Maigatari, Shugaban kungiyar na jihar Malam Nasiru Idris Sara, ya bayyana shugabanci a matsayin rikon amana a maimakon hanyar tara dukiya da alfahari, a don haka akwai bukatar sakataren ya yi aiki tukuru dan kare martabar sana’ar dako da masu yin ta.
Yana mai cewar shugabancin kungiyar zai hada kai da shugabannin kananan hukumomi da masu rike da sarautu da jami’an tsaro a matsayin abokan kawo cigaba wajen daga likkafar sana’ar dako.
Nasiru Idris Sara ya kuma yi kira ga daukacin ‘yan dako a fadin jihar da su yi rijista da kungiyar domin kasacewa a karkashin inuwa daya ta yadda za su ci moriyar tanade tanaden ta, sannan su kasance masu mutunta shugabanci da kuma bin doka da oda domin inganta rayuwar su.
Ya ce yayin da kungiyar ta ke da ‘yan dako kimanin dubu 20 a karkashin ta, akwai bukatar duk ‘yan dakon da ba su da katin zabe su karbi sabo ko kuma su sabunta wanda ya bata ko ya lalace domin amfani da damar su wajen zaben shugabanni.
A sakon sa, Hakimin Maigatari Alhaji Sani Alhassan Muhammad wanda ya sami wakilcin Sarkin Kasuwar Maigatari Alhaji Muhammadu Sarkin Kasuwa, ya bukaci sabon sakataren kungiyar Malam Muhammad Tajudeen ya kasance mai nuna gaskiya da adalci wajen huldar sa da ‘yan dako da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci, inda ya bayyana murnar samun wannan mukamin.
Cikin wadanda suka halarci taron sun hada da Sarkin hatsin Maigatari, Malam Mu’azu Bako da Shugaban leburorin Dingas na Jamhuriyar Nijar Malam Lawwali Hassan.
Usman Mohammed Zaria