Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar
Published: 12th, August 2025 GMT
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayar da gargadi game da hawan keken masu kananan shekaru da rashin biyayya ga fitilun ababen hawa a cikin babban birnin Kano.
Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanya wa hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.
Gargadin na zuwa ne bayan an samu munanan hadurran kan tituna guda 16 a cikin watan Agustan 2025, wanda ya yi sanadin jikkata da asarar dukiyoyi.
Rundunar ta lura cewa hawan keken ƙananan yara yana haifar da babban haɗari ga mahaya da sauran masu amfani da hanyar.
An shawarci iyaye da masu kula da su da su guji barin ‘ya’yansu da ba su da shekaru su yi amfani da keken mai kafa uku, domin hakan zai jawo hukunci mai tsanani a karkashin dokar.
Rundunar ta kuma lura da yanayin rashin biyayya ga fitilun ababen hawa da kuma dokokin hanya daga wasu masu amfani da hanyar.
“Wannan dabi’a tana haifar da cunkoson ababen hawa da ba dole ba, da kuma hadurran da za a iya kaucewa, da jefa rayukan mutane cikin hadari da kuma kawo cikas ga zirga-zirgar ababen hawa.”
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kebe jami’an tsaro domin tabbatar da bin ka’idojin zirga-zirga.
Rundunar ta bukaci duk ‘yan kasar da su bi dokokin hanya da kuma bayar da rahoton duk wani abu na hawan keken kanana, tukin ganganci, ko wasu keta haddi.
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaro na rayuka da dukiyoyi a jihar.
Abdullahi jalaluddeen/Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Fitillun hanya ababen hawa Rundunar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Za a biya ma’aikata 445 garatitun sama da biliyan ɗaya a Kebbi
Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya amince da biyan sama da biliyan ɗaya a matsayin kuɗin garatitu ga iyalan ma’aikatan gwamnati 445 da suka rasu.
Wannan biyan zai shafi tsoffin ma’aikatan jihar, ma’aikatan wucin-gadi, ma’aikatan ƙananan hukumomi, da malaman firamare.
Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfaraAna sa ran biyan kuɗin zai fara daga kan watan Disamba 2024 zuwa Maris ɗin 2025.
Gwamna Idri, ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da kula da walwalar ma’aikata da iyalansu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen yi wa jihar hidima.
Ya ce biyan haƙƙoƙin ma’aikata ba wasa ba ne, kuma gwamnatinsa za ta yi tsayin daka wajen ganin an biya su a kan lokaci.
Wasu tsoffin ma’aikata sun yaba da wannan mataki, amma sun roƙi gwamnan da ya ci gaba da biyan sauran waɗanda ba su shiga jerin wannan sahun ba.
Sun ce akwai ɗimbin masu jiran haƙƙinsu, kuma idan ana biyan kowa a hankali, cikin lokaci kaɗan za a rage yawan masu jiran kuɗi.
Sun kuma buƙaci gwamnati ta duba tsarin fansho na jihar don inganta shi.
A cewarsu, yawancin masu karɓar fansho a Kebbi na cikin halin ƙunci saboda kuɗin da ake ba su ba ya wadatarwa.