Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari
Published: 11th, August 2025 GMT
Jami’an tsaron kasar Iraki sun sanar da gano wata kungiyar ‘yan ta’adda da ta yi niyyar kai wa masu ziyarar Arbaeen hare-hare, wanda aka shirya gudanarwa a kwanaki masu zuwa.
Ma’aikatar tsaron ta bayyana cewa, “tsarin da ‘yan ta’addan ke da shi sun hada da dasa ababen fashewa a kan hanyoyin da masu tattaki ke bi a yankin kudancin kasar da kuma saka guba a cikin kayan abinci da ake ba wa masu tattaki.
Har ila yau, bincike ya nuna cewa kungiyar ta’addanci ta ISIS ta yi amfani da hanyoyi daban-daban wajen daukar wadannan mambobi nata da aka wanke wa kwakwalwa domin aiwatar da wadannan ayyuka.
Ma’aikatar ta bayyana cewa, kungiyar na yin hakan ne ta hanyar yin amfani littafai da aka rubuta musamman domin tunzura masu irin wannan Akida ta kafirta musulmi da zubar da jinni, tare da yin amfani da wasu malamai masu irin waannan Akida domin gurbata tunanin matasa musulmi, da kuma saka su hanyar ta’addanci da sunan addini ko jihadi.
A ranar alhamis din da ta gabata ma karamar hukumar Karbala ta sanar da kame wasu mutane 22 da suke Shirin kai hare-haren ta’addancin da suka tsara a lokacin tarukan ziyarar Arbaeen na wannan shekara.
Ko a shekarun baya an yi ta samun irin wadannan matsaloli na ta’addanci daga kungiyoyi masu dauke da akidar takfir da suke kafirta al’ummar musulmi tare da halasta jininsu, inda suke Kallon dukkanin musulmi da ba su a cikinsu a matsayin ‘yan bidi’a mushrikai ko kafirai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Chadi: An Daure Wani Dan Adawa Shekaru 20 A Gidan Kaso Da tara August 10, 2025 Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin August 10, 2025 Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasus Ko Rasha Bata taimaka ba August 10, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya August 10, 2025 An Zabi Alkalan Wasa Biyu Daga Kasar Iran Don Alkalanci A gasar Kwallon Kafa ta Mata August 10, 2025 Kasar Iran Ta Yi Allah Wadai Da Bukatar ‘Yan Sahayoniyya Ta Son Kwace Zirin Gaza August 10, 2025 Iran Ta Cimma Matsayi A Yaki Kwanaki 12 August 10, 2025 Jami’an Tsaron Iran Sun Murkushe ‘Yan Ta’adda Kan Ofishin ‘Yan Sanda A Kudu Maso Gabashin Kasar August 10, 2025 Jefa Agajin Abinci Ta Sama A Zirin Gaza Ya Janyo Shahadan Falasdinawa 23 Tare Da Jikkata Wasu 124 August 10, 2025 Tehran Times: Mai Yiwuwa Iran da Amurka su koma Tattaunawa August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasusu Ko Rasha Bata taimaka ba
Babban mai bawa jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae shawara, wato Ali Akbar Wilayati ya bayyana cewa Iran zata hana America samar da hanya a yankin Caucasus, ko da kasar rasha ta taimaka ko bata taimaka ba.
A wata hira na musamman da kamfanin dillancin labaran Tasnim, Ali Akbara wailayati ya yi watsi da wani shiri wai shi zangezur wanda an tsara zai hana kasar Armenia da Nakhchivan.
Da aka tambaye shi da maganar cewa Armenia zata bawa Amurka yankin haya na tsawon shekaru 99 masu zuwa, Wilayati ya bayyana cewa warin zai zama makabartan sojojin Donal trump, wannan ba hanya ce wanda Amurka ta mallaka ba.
Ya ce gwamnatin kasar Iran ta sha bayyana cewa bata amince da shirin Zangezur a yankin Caucasusu don yankin yana daga cikin yankuna masu hatsari a duniya. Kuma zai haddasa matsalolin tsaro ga kasr Iran.
Saboda shirin zai rarraba kasashen yakin da kuma batar da kasar Armenia gaba dayanta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya August 10, 2025 An Zabi Alkalan Wasa Biyu Daga Kasar Iran Don Alkalanci A gasar Kwallon Kafa ta Mata August 10, 2025 Kasar Iran Ta Yi Allah Wadai Da Bukatar ‘Yan Sahayoniyya Ta Son Kwace Zirin Gaza August 10, 2025 Iran Ta Cimma Matsayi A Yaki Kwanaki 12 August 10, 2025 Jami’an Tsaron Iran Sun Murkushe ‘Yan Ta’adda Kan Ofishin ‘Yan Sanda A Kudu Maso Gabashin Kasar August 10, 2025 Jefa Agajin Abinci Ta Sama A Zirin Gaza Ya Janyo Shahadan Falasdinawa 23 Tare Da Jikkata Wasu 124 August 10, 2025 Tehran Times: Mai Yiwuwa Iran da Amurka su koma Tattaunawa August 10, 2025 Tel Aviv: Dubban yahudawa sun yi zanga-zangar adawa da yakin Gaza August 10, 2025 Welayati: Makircin Amurka da Isra’ila na kwance damarar Hizbullah ba zai yi nasara ba August 10, 2025 Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci