Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya
Published: 11th, August 2025 GMT
A safiyar wannan Litinin ɗin ce aka wayi gari da wani mummunan hatsarin tankoki biyu na dakon iskar gas a Zariya, inda direba ɗaya kacal ya tsira da rai, yayin da wasu da dama suka ƙone ƙurmus.
Shaidun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe tara na safe, a kusa da shatale-talen Jirgin Sama Mota da ke titin Kaduna zuwa Zariya, daura da sabuwar Kasuwar Ɗan Magaji.
Rahotanni sun nuna cewa motocin biyu sun gogi juna ne yayin da ɗaya ke ƙoƙarin wuce ɗaya, lamarin da ya haddasa kamawar wuta nan take.
An ji wata ƙara mai ƙarfi da ta tashi a lokacin haɗarin, lamarin da ya tayar da hankalin mazauna yankin.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, mutane da dama sun yi ta tserewa daga gidajensu domin guje wa abin da ka iya zuwa ya komo, yayin da kuma hayaƙi mai yawa ya mamaye hanyar da ya daƙile zirga-zirgar ababen hawa.
Jami’an tsaro da na kashe gobara sun kai ɗauki wurin domin ceto mutane, amma ƙarfin wutar ya hana su samun damar kaiwa kan motocin.
Shugaban Sashen Kula da Hatsari na Ƙasa (FRSC) reshen Zariya, Nasir Abdullahi Falgore, ya bayyana cewa hatsarin ya faru ne sakamakon goguwar motocin dakon gas ɗin biyu, saɓanin raɗe-raɗin cewa tsautsayin ya rutsa da wasu ƙananan motoci ƙirar Golf.
“Direban ɗaya daga cikin motocin ya tsira, kuma mun kai shi asibiti domin samun kulawa. Shi kaɗai ne zai iya ba da cikakken bayani idan ya samu sauƙi,” inji Falgore.
Shugaban Ƙungiyar Direbobi a Zariya, Malam Sa’idu Haruna, ya bayyana cewa ana yawan samun hatsari a wurin saboda yanayin kwana da titin yake da shi.
“Kusan duk wata biyu zuwa uku sai an sami hatsari a nan. Muna kira ga hukumomi su kawo ɗauki,” inji shi.
Haka kuma, shugaban bayar da agajin gaggawa na ƙaramar hukumar Sabon Gari, Abdul Malik Aminu, tare da na Zariya, Abdul’muminu Adamu, sun tabbatar da cewa ba a gama tantance adadin mutanen da suka rasu ba saboda akwai fasinjoji a motocin da ba a gano su ba tukuna.
DPO na ofishin Ɗan Magaji, CSP Auwalu A. Sani, ya ce aikinsu shi ne sanya ido don kare rayukan masu wucewa, amma bai bayar da ƙarin bayani kan hatsarin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hatsari iskar gas Motar Dako Zariya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Dr Ali Larijan wanda ya ke ziyarar aiki na kwanaki uku a kasar Pakistan ya yabawa kasar saboda goyon bayan da ta bawa kasarsa a lokacin yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorawa kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Dr Ali Larijana yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Talata. Sannan yace ya isar da sakon gaisuwa na Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khami’ae ga mutanen kasar Pakistan. Banda haka ya gana da Firai ministan kasar Shehbaz Sharif da shugaban kasa Asif Ali Zardari da kuma kakakin majalisar dokokin kasar kasar Sardar Avaz Saadik.
A ganawar Larijani da Sharif sun tattauna kan dangantaka mai tsawo da ke tsakanin Iran da Pakisatan, da kuma bukatar a kara zurfafata.
Sharif a nasa bangaren ya bayyana cewa nan ba da dadewa waministan harkokin wajen kasar Mohammad Ishak Dar zai ziyarci Tehran inda ake saran zai rattaba hannu kan yarjeniyoyi na bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu, daga ciki har da batun kammala aikin shimfida bututun gas daga kasar Iran zuwa Pakistan. Da kuma harkokin sadarwa.
A cikin wannan shekarar ne dai kasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjeniyar bunkasa kasuwanci ta dalar Amurka billion 10 a tsakaninsu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin Lebanon November 26, 2025 Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci