Leadership News Hausa:
2025-08-11@12:16:37 GMT

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

Published: 11th, August 2025 GMT

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

Kungiyar Kwadago da ta ‘yan kasuwa ta Nijeriya (NLC da TUC) reshen jihar Taraba sun bayyana shirin fara yajin aiki tun daga karfe 12 na daren Litinin 11 ga watan Agusta, 2025. Wannan mataki ya biyo bayan sakamakon taron majalisar zartarwa ta jihar da kungiyoyin biyu suka yi a ranar Lahadi a Jalingo, babban birnin jihar Taraba.

A cikin sanarwar da LEADERSHIP ta samu a daren Lahadi mai dauke da sa hannun sakataren kungiyar NLC, Adamu-Buba, da sakatariyar kungiyar TUC, Polina Gani, sun yi kira ga mambobinsu da su ba da hadin kai ga matakin da kungiyoyin suka dauka domin neman hakkokinsu a wurin gwamnatin jihar ta Taraba. Kungiyar kwadagon ta ce, taron ya sake duba wa’adin da aka bayar tun da farko ga gwamnati game da “ayyukan kwamitin tattara bayanan ma’aikata a na’ura ta hanyar amfani da yatsu da kuma rahoton da kwamitin ya bayar”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Soja ya soka wa ɗan sanda wuƙa har Lahira a Taraba

Wani kurtun soja ya soka wani ɗan sanda mai mukamin Constable, Aaron John da wuƙa har lahira a garin Jalingo, hedikwatar Jihar Taraba.

Kakakin ’yan sanda na jihar, James Lashen, ya ce wannan mummunan al’amari ya faru ne da misalin karfe 9 na dare a ranar Litinin, a unguwar Mayo-Goyi, da ke gefen birnin Jalingo.

Lashen ya bayyana cewa marigayi John ya samu kiran gaggawa daga wasu mazauna yankin dangane da sabani da suka samu da sojan.

A yayin da yake kokarin warware rikicin, sai sojan mai suna Dauda Dedan, ya soka masa wuƙa.

Ya ce, “Mun samu rahoton lamarin daga hedikwatar Brigade ta 6 ta Rundunar Sojin Najeriya, da tabbacin cewa za a kamo sojan da ya tsere domin fuskantar hukunci,” in ji Lashen.

Ya ƙara da cewa rundunar soji ta fara bincike kan lamarin, tare da tabbatar wa ’yan sanda cewa za su haɗa kai wajen kamo wanda ake zargi.

“Sojoji da ’yan sanda na aiki tare. Mun kai ziyara har gidan sojan, kuma za mu tabbatar an kama shi domin ya fuskanci hukunci daidai da abin da ya aikata,” in ji Lashen.

Ya jaddada cewa dangantaka tsakanin sojoji da ’yan sanda a jihar Taraba tana da kyau kuma babu wata matsala a tsakaninsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • An Yi Allah Wadai Da Hana Amfani Da Hijabi A Jami’ar LandMark, Omu-Aran Kwara
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • Dan wasan Barcelona Inigo Martinez ya koma Al-Nassr
  • ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki
  • Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
  • Soja ya soka wa ɗan sanda wuƙa har Lahira a Taraba
  • Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 
  • Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu