Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC) murna bisa ci gaba da riƙe matsayin Maturity Level 3 (ML3) na Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) wajen kula da magunguna da rigakafi.

Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Bayani da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, a cikin wata sanarwa, ya bayyana cewa, an gudanar da binciken sake tantance matsayin WHO daga 28 zuwa 30 ga Mayu, 2025, inda aka kimanta NAFDAC bisa ka’idojin ƙasa da ƙasa.

Hukumar ta fara samun wannan matsayi na ML3 ne a 2022, inda ta zama hukumar farko a Afrika mai kula da ƙasashen da ba sa samar da magunguna da ta cimma wannan nasara.

Wannan sabon tantancewa ya biyo bayan wani binciken ne  a watan Nuwamban 2024, tare da gudanar da tarukan duba Shirin Cigaban Cibiyoyi(IDP) guda biyar tsakanin Fabrairu zuwa Afriln 2025 domin tantance matakan gyara. WHO ta yaba wa NAFDAC kan ci gaba da samun tsari mai ƙarfi, da ke aiki yadda ya kamata, tare da yaba wa goyon bayan gwamnati wajen ƙarfafa hukumar.

Shugaba Tinubu ya jinjina wa shugabanni da ma’aikatan NAFDAC bisa ƙwarewa da sadaukarwa, yana mai cewa wannan nasara ta ƙara ɗaukaka matsayin Najeriya a fannin kula da  lafiya da shirin kare cututtuka.

Ya ce wannan nasara na daidai da kudirin gwamnatinsa na Renewed Hope Agenda domin sauya tsarin kula da lafiya.

Shugaban ya yi nuni da ci gaba da ake samu, ciki har da inganta  cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko 17,000, kyautata kulawa da mata masu juna biyu da na’urorin gano cututtuka a yankunan da ba su da iisassun kayayyakin kula da lafiya, horar da ma’aikatan lafiya 120,000, da kuma ninka yawan masu amfani da shirin  inshorar lafiya na ƙasa cikin shekaru uku.

Ya kuma tabbatar da aniyarsa ta ƙarfafa samar da kayayyakin kiwon lafiya a cikin gida da jawo ra’ayin masu zuba jari a fannin lafiya.

Tinubu ya yi alkawarin ci gaba da tallafa wa NAFDAC a yunkurinta na cimma matsayin WHO Maturity Level 4, mafi girma a duniya kan ingancin sarin kula da magunguna.

 

Daga Bello Wakili

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

Ministar wadda ta je kamfanin domin daukar sabuwar motarta ta alfarma kirar Nord Demir SUB da kamfanin ya hada nataimakin Shugaban jami’ar na sashen kula da ilimi da gudanar da bincike Farfesa Bola Oboh da kuma Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi ne, suka karbi bakuncinta.

 

A jawabin da ta gabatar a lokacin ziyarar ministar ta bayyana cewa,Duba da yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci wajen fitar da kaya zuwa ketare kamfanin zai iya yin amfani da wannan samar waken fitar da motocinsa zuwa ketare.

 

Ta kara da cewa, Nijeriya na da gurare biyu ne da ake hada motoci da suka hada da, na wannan jami’ar da kuma na EPs, inda ta yi nuni da cewa, karfin da kamfanin ya ke da shi, zai iya cike gibin bukatar da ake da ita, ta ‘yan kasar na bukatar motocin.

 

Ya ci gaba da cewa, za mu ci gaba da kara karfafa kwarin guwair ‘yan kasar domin da kuma sauran kamfanoni masu zaman kansu domin su rinka sayen kayan da kamfanonin kasar, suka sarrafa da kuma hada su.

 

Ta ce, wannan babban abin alhari ne, ganin cewa, a wannan jami’ar ce, aka hada wannan mortar.

 

Shi kuwa a na sa jawabin Farfesa Oboh ya bayyana cewa, muna Myrna da wannan shirin na Gwamnatin Tarayya wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ke jagorantar bai wa ‘yan kasar kwarin guwair sayen kayan da aka sarrafa a cikin kasar

A cewarsa, jami’ar ta UNILAG, ba wai kawai na yin alfahari da samun wannan wajen hada motocin ba ne, kadai amma ta na alharin da cewa, an samar da wajen a jami’ar.

Shi ma, Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi, a yayin da ya ke nuna jin dadinsa kan gudunmwar da ministar ke bai wa kamfanin ya a bayyana cewa, na yi matukar farin ciki ganin cewa, ministar ta kasance daya daga cikin abokan cinikayyar mu

Kazalika, Shugaban ya kuma gode wa mahukunta jami’ar ta UNILAG kan yin hadaka da kamfanin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho October 10, 2025 Tattalin Arziki An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi  October 10, 2025 Tattalin Arziki Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Cibiyar Lafiya Ta Nasser Ta Ce: Yaran Gaza 5,500 Suna Bukatar Agajin Gaggawa A Kasashen Waje
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a Masar ranar Litinin  
  • Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza
  • Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga Dan Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya.
  • Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza
  • Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida