Aminiya:
2025-09-24@11:17:04 GMT

Al’ummar Zamfara: ’Yan bindiga sun karɓi N56m domin izinin yin noma

Published: 7th, August 2025 GMT

Manoman gundumar Ɗan Isa da ke Ƙaramar hukumar Kaura Namoda a Jihar Zamfara sun ce ’yan bindiga sun yi musu barazana a wannan damina ta bana.

Da yake tabbatar da hakan ga Daily Trust a wata tattaunawa ta wayar tarho, Hakimin unguwar Malam Hassan Yarima, ya ce kowane ƙauyuka 35 da ke ƙarkashin gundumarsa ya biya Naira dubu 800 kafin a bar mazauna yankin su yi noma.

NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026 ’Yan sanda sun ƙwato jariri da aka sace a asibitin Ekiti

“Kowanne ƙauye kuma zai sake biyan Naira dubu 800, don bai wa mazauna yankin damar girbe amfanin gonakinsu, wannan ita ce yarjejeniya da muka cimma da shugaban ’yan bindiga da ke kula da wannan yanki, Ɗan Sadiya.”

“Ina magana ne game da gundumata kawai, ban san abin da mazauna wasu gundumomi suka biya wa ’yan bindigar ba a wannan shekara. Amma wani abu da nake da tabbacin shi ne mazauna yankin su biya kafin a barsu su yi noma.

“Ba mu da wani zaɓi illa mu bi umarninsa, in ba haka ba, ’yan bindiga ba za su barmu mu yi noman gonakinmu ba, a ƙalla idan muka yi noma, za mu iya samun wani abu ga iyalanmu,” in ji shi.

Sai dai Yarima ya koka da cewa, duk da biyan kuɗin noma, har yanzu ’yan bindiga sun mamaye ƙauyukansu suna sace dabbobi tare da kwashe kayan abinci.

Ya yi nadama kan yadda mazauna unguwannin da abin ya shafa suke yin amfani da duk abin da suke da shi a ƙoƙarin samun zaman lafiya da ’yan bindigar.

“Muna so mu zauna lafiya da ’yan bindigar, amma gaskiya sun karɓe mana komai, sun yi awon gaba da dabbobinmu sun kwashe kuɗinmu, amfanin noma  da sauran kayayyaki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kaura Namoda Manoman gundumar Ɗan Isa Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Duk da amfanin kifi ga lafiyar jikin mutum da kuma samar da kudin shiga masana sun ce ba a amfani da shi yadda ya kamata a Najeriya.

 

Baya ga bai wa jiki lafiya, kifi  ka iya samar da kudaden shiga ga daidaikun ’yan Najeriya da ma kasar gaba daya.

NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa ’yan Najeriya basa samun cin kifi kamar yadda ya kamata.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Imam Khamenei: Hadin kan al’ummar Iran a yakin kwanaki 12 ya sanya makiya kunya
  • DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • ’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a Kebbi
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja
  • Mahara sun kashe ’yan sanda a shingen bincike a Kogi
  • Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja
  • An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina