Al’ummar Zamfara: ’Yan bindiga sun karɓi N56m domin izinin yin noma
Published: 7th, August 2025 GMT
Manoman gundumar Ɗan Isa da ke Ƙaramar hukumar Kaura Namoda a Jihar Zamfara sun ce ’yan bindiga sun yi musu barazana a wannan damina ta bana.
Da yake tabbatar da hakan ga Daily Trust a wata tattaunawa ta wayar tarho, Hakimin unguwar Malam Hassan Yarima, ya ce kowane ƙauyuka 35 da ke ƙarkashin gundumarsa ya biya Naira dubu 800 kafin a bar mazauna yankin su yi noma.
“Kowanne ƙauye kuma zai sake biyan Naira dubu 800, don bai wa mazauna yankin damar girbe amfanin gonakinsu, wannan ita ce yarjejeniya da muka cimma da shugaban ’yan bindiga da ke kula da wannan yanki, Ɗan Sadiya.”
“Ina magana ne game da gundumata kawai, ban san abin da mazauna wasu gundumomi suka biya wa ’yan bindigar ba a wannan shekara. Amma wani abu da nake da tabbacin shi ne mazauna yankin su biya kafin a barsu su yi noma.
“Ba mu da wani zaɓi illa mu bi umarninsa, in ba haka ba, ’yan bindiga ba za su barmu mu yi noman gonakinmu ba, a ƙalla idan muka yi noma, za mu iya samun wani abu ga iyalanmu,” in ji shi.
Sai dai Yarima ya koka da cewa, duk da biyan kuɗin noma, har yanzu ’yan bindiga sun mamaye ƙauyukansu suna sace dabbobi tare da kwashe kayan abinci.
Ya yi nadama kan yadda mazauna unguwannin da abin ya shafa suke yin amfani da duk abin da suke da shi a ƙoƙarin samun zaman lafiya da ’yan bindigar.
“Muna so mu zauna lafiya da ’yan bindigar, amma gaskiya sun karɓe mana komai, sun yi awon gaba da dabbobinmu sun kwashe kuɗinmu, amfanin noma da sauran kayayyaki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kaura Namoda Manoman gundumar Ɗan Isa Zamfara yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
Yau 7 ga watan Nuwamba, Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taya Paul Biya murnar yin tazarce a wani sabon wa’adin shugabancin kasar Kamaru.
Shugaba Xi ya ce, kasar Sin da Kamaru suna da daddadiyar alaka mai kyau. A cikin ‘yan shekarun nan, amincewar siyasa tsakanin kasashen biyu ta kara zurfafawa, kuma an samu nasarori masu yawa a fannoni daban-daban na hadin gwiwa, tare da mara wa juna goyon baya a kan batutuwan da suka shafi muradunsu da kuma batutuwa masu muhimmanci.
A shekara mai zuwa ce za a cika shekaru 55 da kulla alakar diflomasiyya tsakanin kasar Sin da Kamaru, matakin da ya samar musu da sabbin damammaki na ci gaban huldarsu. Xi yana dora muhimmanci sosai kan ci gaban dangantakar Sin da Kamaru, kuma yana fatan hadin gwiwa da shugaba Paul Biya, don aiwatar da sakamakon taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka gudanar a birnin Beijing a bara, ta yadda za a inganta cikakkiyar alaka ta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare masu zurfi, da kyautata rayuwar al’ummomin kasashen biyu. (Amina Xu)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA