Aminiya:
2025-09-24@11:21:14 GMT

Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano

Published: 8th, August 2025 GMT

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana alhini kan rasuwar Sadiq Gentle, wani hadiminsa kan harkokin yada labarai a Ma’aikatar Tarihi da Al’adu ta jihar, wanda wasu da ake zargi ’yan daba suka kai masa harin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya wallafa a Facebook, ta bayyana Sadiq a matsayin jarumi, ƙwararre, kuma mai kishin kasa a fannin kafafen sada zumunta.

NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026 An kashe mutum huɗu da tayar da ƙauyuka 17 a Sakkwato

Gwamna Abba ya ce mutuwar Sadiq Gentle ta girgiza shi sosai, inda ya bayyana mamacin a matsayin mutum mai kamun kai, haƙuri, da sadaukarwa ga ci gaban Jihar Kano.

Gwamnan ya bayyana kisan da aka yi masa a matsayin keta haddin bil’adama da ba za a lamunta ba, lamarin da bayyana a matsayin ƙoƙarin da wasu bata-gari ke yi domin kawo cikas a zaman lafiya a jihar.

Ya umarci hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike, tare da tabbatar da cewa wadanda suka aikata wannan aika-aikar sun fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

Ya kuma jaddada cewa gwamnatin jihar ba za ta lamunci irin wannan ta’asa ba, yana mai bayyana bukatar tsauraran matakan tsaro domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kazalika, Gwamnan ya mika ta’aziyya ga iyalan marigayin, abokan aikinsa, da daukacin jami’an Ma’aikatan Tarihi da Al’adu, yana mai tabbatar musu da cewa Gwamnatin Kano na tare da su a wannan lokaci na jimami da baƙin ciki.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne wasu da ake zargi ’yan daba ne suka sassari hadimin gwamnan yayin wani farmaki da suka kai masa har gida da adduna.

Daga bisani an garzaya da Sadiq Gentle Asibitin Murtala da ke birnin Kano inda a nan ajali ya katse masa hanzari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

An kama ɗan sandan bogi a Kano

Rundunar ’yan sanda a Jihar Kano ta sanar da cafke wani mutum da ke yi mata sojan-gona yana yaudarar jama’a domin karɓar musu kuɗi.

An cafke wanda ake zargin ne a ranar Lahadi, 21 ga Satumbar 2025 a yankin Kofar Dawanau, sanye da kayan ’yan sanda, wanda bayanai suka ce ya daɗe yana aika-aikar.

An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa

Sanawar da rundunar ta fitar ta bayyana cewe an kama shi ne bayan da jama’a suka shigar da ƙorafe-ƙorafe da dama game da ayyukan wasu da ke yin kutse da shigar ’yan sanda domin damfarar jama’a.

Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce “binciken farko ya tabbatar cewa wanda ake zargin ba ɗan sanda ba ne, kuma ba shi da alaƙa da rundunar kwata-kwata.”

A wata hira da rundunar ta yi da mutumin wanda mazaunin Kofar Waika ne, ya ce sha’awar aikin ce ta sanya yake yi wa ’yan sandan sojan gona, inda yake bayar da hannu a kan titi domin samun na ɓatarwa.

Ya shaida cewa shaye-shayen da yake yi bai wuce na sigari da tabar wiwi ba, inda ya nemi a yi masa afuwa duk da ya nanata cewa duk duniya babu aikin da yake sha’awa kamar aikin ’yan sanda tare da neman a taimaka a dauke shi aikin.

Kazalika, ya bayyana cewa muradin ganin ya zama ɗan ya sanya shi sake aikata wannan laifi na sojan-gona duk da an taɓa kama shi da laifin a baya.

Tuni dai rundunar ta bayyana cewa za a gurfanar da shi a gaban kotu domin fuskantar hukunci bayan kammala bincike.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bukaci jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai ko ƙorafe-ƙorafe idan sun san wani abu game da wanda ake zargi ko makamantansa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗan sandan bogi a Kano
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • Mahara sun kashe ɗan sanda, sun ɗauke bindigarsa a Taraba
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • DSS ta yi wa Malami tambayoyi kan harin da aka kai masa a Kebbi
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ribas, Fubara Ya Ziyarci Tinubu A Fadar Gwamnati A Abuja
  • Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro