NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Published: 10th, August 2025 GMT
Ya ƙara da cewa an kama aƙalla mutane uku da ake zargin suna da alaƙa da kayan a wani samame da aka kai musu.
Babafemi ya ce, “Kashi na farko na kayan, wanda ya kunshi kwayoyin Tramadol 57,420 na tramadol 225mg da 57 na hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1.60, an kama su ne a cikin wani kaya da zai je kasar Gabon a Air Cote d’Iɓoire a ranar Asabar, 19 ga watan Yuli, 2025.
“An gano fakiti 11 na hodar iblis da nauyinsu ya kai kilogiram 1 daga baya daga wasu madubi guda hudu da ake shiryawa don fitar da su zuwa kasashen waje, wadanda aka gano a gidan Uzochukwu a ranar Litinin, 21 ga watan Yuli, wanda ya kawo adadin hodar iblis zuwa 68 mai nauyin kilogiram 2.60.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram a Borno
Dakarun Sojin Najeriya sun kashe wani babban Kwamandan Boko Haram, mai suna Abu Nasr, wanda ya jagoranci kai hari garin Rann, da ke Ƙaramar Hukumar Kala Balge, a Jihar Borno.
A makon da ya gabata, dakarun rundunar Operation Hadin Kai, sun daƙile harin da Boko Haram suka kai garin Rann.
Jarumar Kannywood Rahama Sadau ta yi aure Za a biya ma’aikata 445 garatutin sama da biliyan ɗaya a KebbiSun kashe ’yan ta’adda da dama, duk da cewa sojoji biyu sun rasa rayukansu sakamakon harba roka da ‘yan ta’addan suka yi.
Rann na da iyaka da ƙasar Kamaru, kuma daga Maiduguri yana da nisa kusan kilomita 196.
Bayanan jami’an tsaro sun tabbatar cewa Abu Nasr, wanda ya jagoranci tawagarsa zuwa Rann daga Kamaru, ya mutu tare da wasu ’yan ta’addan.
An kuma samu nasarar ƙwato bindigogi, harsasai, bama-baman roka da sauran abubuwan fashewa.
Harin ya faru daga ranar Alhamis, 7 ga watan Agusta, zuwa safiyar Juma’a, 8 ga watan Agusta, 2025, tare da taimakon bayan jiragen sojojin sama.
A cewar jami’an tsaro, an gano gawarwakin ’yan ta’adda bakwai a wajen, kuma akwai yiwuwar sama da hakan sun rasu.