Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfara
Published: 9th, August 2025 GMT
Wata babbar kotu a Jihar Borno, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Aisha Kumaliya, ta yanke wa Kalthum Mustapha hukuncin ɗaurin shekara uku a gidan gyaran hali bayan samun ta da laifin aikata damfara.
Hukumar EFCC ta bayyana cewa, an fara gurfanar da Kalthum a ranar 13 ga watan Mayu, 2024.
Tsohon Ministan Noma Audu Ogbeh ya rasu Fashewar gurneti ya kashe yara uku a BornoAna tuhumarta da karɓar kuɗi Naira miliyan 1.
Sai dai ba ta kawo kayan ba kuma ba ta mayar musu da kuɗinsu ba.
A lokacin shari’ar, lauyoyin masu shigar da ƙara, Mukhtar Ali Ahmed da Faruku Muhammad, sun gabatar da shaidu da hujjoji.
Mai shari’a ta kuma bai wa Kalthum zaɓin biya tara ta Naira 50,000 maimakon zaman watanni shida a gidan gyaran hali.
Bugu da ƙari, kotun ta umarce ta da ta biya Naira 635,000 a matsayin diyya ga waɗanda ta damfara.
Idan kuma ta gaza biyan diyyar, za ta ƙara fuskantar ɗaurin shekaru biyu a kan waɗanda aka yi mata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Damfara diyya ɗauri Tara
এছাড়াও পড়ুন:
Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan
Tarayyar turai ta bayyana cewa ma’aikatan Agaji ba za su iya isha cikin garin Al-fahar ba,kuma birnin ya zama tamkar makabarta.
Tarayyar turai din ta bakin mai Magana da yawunta Eva Herneserova ta kuma ce; Sudan ta zama daya daga cikin kasashen da gudanar da ayyukan agaji ya tsananta a duniya,kuma har yanzu da akwai fararen hula da aka killace su adaidai lokacin da ake ci gaba da kai wa asibitoci hare-hare.
Eva Herneserova ta kuma ce; Babu sauki ko kadan a kokarin shiga cikin birnin domin isar da kayan agaji.
Ma Magana da yawun kungiyar tarayyar turai din ta kuma yi gagradi akan cewa bai kamata a rika amfani da yunwa da kuma kisan kiyashi a matsayin makamin yaki ba,domin hakan yana a matsayin take dokokin kasa da kasa ne na ayyukan agaji.
Haka nan kuma ta yi kira ga dukkanin bangarorin da suke fada da juna da koma kan teburin tattaunawa da kuma tsagaita wutar yaki.
Rundunar kai daukin gaggawa ta RSF kwace iko da birnin Al-fasha, bayan da killace shi na tsawon watanni 18. A yayin da mayana rundunar ta RSF su ka shiga cikin birnin sun aikata laifukan yaki da ya hada da yi wa fararen hula kisan kiyashi.
Bugu da kari, suna hana mutane ficewa daga cikin garin domin zuwa inda za su sami aminci.
Gwamnatin Sudan tana zargin kasar UAE da taimakawa mayakan na RSF da makamai da kuma kawo ‘yan ina da yaki daga kasashen Columbia, Sudan Ta Kudu da Afirka Ta Tsakiya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon November 7, 2025 Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Falasdinawa Miliyan 1.5 Ne Ke Cikin Mawuyacin Hali November 7, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya November 7, 2025 Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar November 7, 2025 An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar November 7, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jinin Isra’ila . November 7, 2025 Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne November 7, 2025 Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar November 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci