Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kaddamar Da Tantance Malamai Da Ma’aikatan Lafiya
Published: 10th, August 2025 GMT
A kokarin ta na ci gaba da kula da harkokin ilimi a yankin, Karamar Hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa ta kaddamar da aikin tantance malaman makaranta na B teach da kuma ma’aikatan lafiya na wato B health.
A jawabin sa wajen fara tantance malaman da ma’aikatan lafiyar, Shugaban karamar hukumar, Dr Muhammad Uba Builder, yace aikin tantancewar ya zama wajibi domin tabbatar da ma’aikata na gaskiya da kuma gano na bogi.
Yana mai cewar akwai rahotannin daya nuna wasu suna aiki 2 wasu kuma suna amfani da takardun bogi.
A don haka, yace duk wanda aka samu da hakan zai rasa aikin sa gami da kama shi don fuskantar hukunci.
Builder Muhammad Uba, yace an ware ranar asabar domin tantance malaman da kuma ma’aikatan lafiya domin tabbatar na gaskiya da adalci.
Yayi nuni da cewar, duk malamin da aka samu da takardun bogi, shakka babu za’a maye gurbin sa da wani.
Kazakika, Builder yaja hakalin su da su kasance masu tsoran Allah wajen gudanar da aikin su tare da ganin suna zuwa wuraren ayyukansu akan lokaci.
A jawabin sa, kansila mai gafaka na sashen ayyuka na karamar hukumar, Malam Haladu Maigari ya zayyana ayyukan raya kasa da shugaban karamar hukumar ya aiwatar karkashin jagorancin Builder Muhammad Uba.
Ya kuma baiwa malaman da ma’aikatan lafiyan shawarar fadin gaskiya na al’amurran su.
A jawaban su, jami’in shirin B Teach, Malam Nazifi Bala da kuma jami’in shirin B Health Malam mujitafa Ibrahim sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa kokarin sa na rage zaman kashe wando ga matasan yankin karamar hukumar ta Birnin kudu.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa
A yau Jumma’a 10 ga watan Oktoba, an kaddamar da wani shiri na aikin hadin gwiwa mai lakabin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” na rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) na shekarar 2026 a birnin Beijing.
Shen Haixiong, babban darektan CMG, ya gabatar da jawabi a wajen taron, inda ya bayyana cewa, CMG ya samu damar zamowa kan gaba a fagen yada labarai na kasa da kasa bisa kayayyakin aiki da ma’aikata, kuma shi ne muhimmin dandali na tallata kayayyakin kasar Sin. Kamfanin a shirye yake ya dauki shirin a matsayin wata damar yin aiki kafada da kafada da abokan kawance daga kowane bangare na rayuwa, tare da rubuta sabon babi a fagen gina kasa mai kunshe da kayayyakin kamfanonin da suka kasance a kan gaba. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA