An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
Published: 11th, August 2025 GMT
’Yan ta’adda sun kashe mutum 24 tare da sace wasu akalla 144 a cikin mako guda a sassan Jihar Zamfara.
Kungiyar Al’ummar Zamfara mai suna Zamfara Zamfara Circle Community Initiative ta bayyana cewa ’yan ta’addan sun kai hare-haren da suka kai kan kauyuka 15 inda suka jikkata mutane 16 a kananan hukumomi daban-daban.
Ta bayyana cewa daga ranar 4 zuwa 10 ga watan nan na Agusta, 2025 ’yan ta’adda suka kai hare haren; kauyukan da aka kai wa farmakin sun hada da Sabe, Tungar Yamma, Sauru, Lambasu, Dogon Madacci, Dankalgo, da Kwanar Kalgo a ƙaramar hukumar Bakura.
A Karamar Hukumar Tsafe, hare-haren sun shafi Chediya, Kucheri, Yankuzo, da Katangar Gabas Bilbils.
A Karamar hukumar Mafara, an samu rahoton hare-hare a Tabkin Rama, Matsafa, da Ruwan Gizo, yayin da Rafin Jema a Gummi da ƙauyukan Adabka da Masu a Bukkuyum suma suka fuskanci hari.
Kungiyar ta jaddada cewa ci gaba da kai hare-hare yana nuna bukatar gaggawa ta ƙarfafa matakan tsaro domin kare al’ummomin karkara daga hannun ‘yan bindiga da ke addabar jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane hare hare Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta October 11, 2025
Tsaro Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara October 5, 2025
Tsaro Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ October 4, 2025