Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.
Published: 18th, April 2025 GMT
Gwamnatin jihar Neja za ta fara gudanar da zirga-zirgar jiragen sama daga sabon filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu da aka kaddamar a Minna, tare da kamfanin Overland Airways Limited.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban jami’in kula da zirga-zirgar jiragen sama na Overland, Captain Edward Boyo ya raba wa manema labarai a Minna, babban birnin jihar Neja.
Ya bayyana cewa an shirya fara jigilar jiragen a ranar 23 ga Afrilu, 2025, wanda zai hada Minna zuwa Abuja da Legas, manyan biranen siyasa da kasuwanci na Najeriya.
Kyaftin Boyo ya bayyana cewa, haɗin gwiwa da kamfanin na Overland Airways—kamfanin jiragen sama masu zaman kansu mafi dadewa a Najeriya—yana wakiltar wani muhimmin ci gaba na aiwatar da tsarin raya ababen more rayuwa na Gwamna Bago da kuma sanya jihar Neja a matsayin cibiyar sa hannun jari, kasuwanci, da yawon buɗe ido.
“Mun yi farin cikin zabar mu a matsayin kamfanin da zai kaddamar da wannan aiki mai dimbin tarihi, “Wannan hidimar tana kara jaddada kudurinmu na fadada hanyoyin sadarwa a fadin Najeriya da kuma hada hannu da gwamnatoci masu hangen nesa kamar jihar Neja domin kawo ci gaba kusa da jama’a, saboda haka muna jinjina wa Gwamna Bago da tawagar NNA kan wannan jajircewa da kawo sauyi.” Ya bayyana.
Tun da farko, babban jami’in gudanarwa na hukumar ta NNA, Alhaji Liman Katamba Kutigi ya ce, “Wannan shirin ya wuce hanyar jirgin sama— gada ce ta samun dama. Ta hanyar hada kai da kamfanin jiragen sama na Overland, muna kafa wani sabon tsari na hada-hadar zirga-zirgar jiragen sama na yankin, tare da aminci da tasirin tattalin arziki.
A cewarsa, wannan shi ne mafarin babban ajandar mayar da jihar Neja a matsayin wata babbar mai taka rawa a harkokin sufurin jiragen sama da na Najeriya.”
A cewar tsare-tsare Tsarin Jirgin kamar haka; Minna – Lagos – Minna: Litinin, Laraba, Juma’a, yayin da ita
Tashi daga Legas zuwa Minna: 8:00 na safe
Tashi daga Minna zuwa Legas: 3:00 na yamma
Minna – Abuja – Minna: Litinin, Laraba, Juma’a da kuma tashi daga Minna zuwa Abuja: 9:30 na safe haka kuma ya tashi daga Abuja zuwa Minna: 2:00 na rana.
Saboda haka, Overland Airways an san shi da kyakkyawan yanayin tafiye-tafiye na yanki, zai yi amfani da waɗannan jiragen ta hanyar amfani da sabon jirginsa na Embraer E-175, kuma kamfanin jirgin ya kiyaye IATA Operational Safety Audit (IOSA) rajista tun 2015 kuma yana aiki da rundunar jiragen ruwa da suka haɗa da Embraer jets, ATR-42s, ATR-42s, ATR-72s da kuma ATR-70D.
PR ALIYU LAWAL.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: jiragen sama
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Taron kaddamar da rabar da taraktocin noman, ya gudana ne a Shalkwatar Ma’aikatar Kula da Aikin noma da kuma yin Noman Rani da ke garin Kalaba.
Kazalika, taron ya samu halartar ‘yan Majalisa da Sarakunan Gargajiya da kungiyoyin manoma mata da masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma da ke jihar da abokan hadaka.
Daukacinsu, sun jinjina wa wannan kokari na gwamna Bassey, kan wannan hangen nesa da gwamnatinsa ta yi, na kaddamar da taraktocin noman, musamman domin ciyar da fannin aikin noman jihar gaba, duba da cewa; fannin ne kinshikin tattalin arzikin jihar.
Har ila yau, gwamna Bassey, ya nanata kudurin gwamnatinsa wajen ci gaba da bai wa fannin aikin noma muhimmanci a matsayin fannin da ke kara habaka tattalin arzikin jihar.
“A lokacin da na karbi jan ragamar shugabancin jihar, mun samar da dabaru da kuma daukar matakai daban-daban, domin kara habaka fannin,“ in ji gwamna Bassey.
“Biyo bayan wata ganawa da muka yi da manoman da ke daukacin kananan hukumominmu, mun gano cewa; kalubalen da suke fuskanta sama da kashi 70 cikin dari, na shiye-shiyen share gonakansu ne, domin fara noma su; saboda kudaden da suke kashewa masu yawa, wajen gyaran gonakin nasu, muna da yakinin wannan shirin zai magance wadannan matsaloi,” a cewar gwamnan.
Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; wannan rabar da taraktocin noma, wadanda ba sa shan man sosai, an tsara su ne kan yadda manoma za su yi gyaran gonakinsu cikin sauki tare kuma da rage musu kashe kudade masu yawa da kuma kara habaka fannin na aikin noma.
“Kashi 108 na kashin farko na shirin, an raba wa manoman jihar jimillar taraktocin noma 324, wadanda kuma aka rabar da su a daukacin fadin jihar,“ a cewar gwamnan.
Gwamna Bassey ya ci gaba da cewa, za a ci gaba da kula da taraktocin ne a karkashin tsarin kungiyoyin manoma na jihar.
“Hakan zai bai wa wadanda suka amfana da taraktocin damar daukar nauyin ci gaba da kula da su, wanda kuma sauran manoman da ke karkara a jihar, su ma za su samu damar samun taraktocin,” in ji shi.
“Ta wannan hanyar, za mu samu damar cin gajiyar da ke fannin noma na jihar, wanda hakan zai kuma bai wa manoman jihar kara dagewa, domin yin noma da samun kudaden shiga da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar,” a cewar tasa.
Kazalika, gwamnan ya kuma zayyano wasu ayyukan noma da gwamnatinsa ta kaddamar da su da suka hada da na samar da Irin noman Rogo, aikin noman Masara da na Waken Soya da sauransu.
Ya bayyana cewa, gwamnatin na kuma ci gaba da habaka samar da Irin Farin Wake da rabar da kayan aikin noma ga kananan manoma tare da kuma shirye-shiyen noman Koko (Cocoa) da Ganyen Shayi, wanda za gudanar ta hanyar yin hadaka da gwamnatin da kuma ‘yan kasuwa.
“Kaddamar da rabar da wadannan taraktocin noman, na daya daga cikin kason farko na kudurin gwamnatinmu na bunkasa fannin aikin noma na jihar, musamman ta hanyar yin amfani da kayan aikin noma na zamani,” in ji gwamnan.
Shi ma, shugaban kamfanin da ya yi kwangilar kawo taraktocin, Femi Odeshirin, ya yaba wa shirin, wanda ya ce; hakan zai kara bunkasa fannin aikin noma na jihar.
“Ba wai kawai rabar da wadannan taraktocin noma ga manoman jihar ba ne da gwamnan ya yi ba, hakan zai kuma kara inganta rayuwar manoman da suka amfana,” in ji Odeleye.
Ya bayyana cewa, kamfanin na kuma kan shirin kafa masana’antar da ake hada taraktocin noma a garin Kalaba da ke jihar, inda masana’antar za ta samar da ayyukan yi sama da 2,000.
Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa (AFAN) reshen jihar, Ojikpong Nyiam Bisong, danganta salon shugabancin gwamna Bassey ya yi da na marigayi tsohon Firimiyan Kudancin Nijeriya, Dakta Michael Okpara.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA