Leadership News Hausa:
2025-09-24@15:43:01 GMT

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Published: 9th, August 2025 GMT

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Ganawar da shugaba Trump ya yi a baya-bayan nan da shugabannin wasu ƙasashe biyar dake nahiyar Afirka, ita ma ta janyo hankalin al’ummun duniya. Inda shugaba Trump ya yabawa shugaban ƙasar Laberiya Joseph Boakai kan yadda ya iya Turancin Ingilishi sosai, lamarin da ya bayyana rashin fahimtarsa kan alaƙar tarihi tsakanin ƙasar Laberiya da Amurka.

Bugu da ƙari, Trump ya katse maganar shugaban Ƙasar Mauritaniya Mohammed Ghazouani, inda ya nemi ya yi magana da sauri.

A hakika, rashin mutuntawa da shugaba Trump ya nuna a fili, ta bayyana ainihin dalilin da ya sa aka gayyaci shugabannin Afirka biyar zuwa wajen ganawar, ba domin neman ƙarfafa dangantaka ba ne, sai dai don tabbatar wa Amurka ɗin damar samun ma’adanan da take buƙata, da yiwuwar sanya waɗannan ƙasashen dake nahiyar Afirka amincewa da karɓar baƙin haure da ake korarsu daga Amurka.

Wataƙila, shugaba Trump ba ya mai da hankali sosai kan ɗa’a a fannin diflomasiyya, amma idan aka kwatanta da shugabannin ƙasar Amurka da suka gabace shi, to, a ƙalla yana bayyana komai a fili ba tare da rufa-rufa ba.

Maganarsa da matakan da ya ɗauka, dukkansu na isar da saƙo zuwa ga ƙasashen Afirka cewa: “Ba ku cikin jerin fannonin da Amurka take nunawa fifiko.”

“Za mu iya musayar wasu abubuwa, amma kada ku yi tsammanin za ku samu riba ko alfanu sosai.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai

Majalisar Wakilai ta bayyana cewa ta amince da duk wasu tsare-tsare da dabarun karɓo rancen kuɗaɗe na Shugaba Bola Tinubu, bisa la’akari da ƙoƙarin da yake yi na farfaɗo da tattalin arziki da kuma rage talauci a ƙasar nan.

Shugaban Majalisar, Abbas Tajudeen ne ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi ranar Litinin, a taron shekara-shekara karo na takwas kan bitar kasafin kuɗaɗe na majalisun dokokin nahiyyar Afirka (African Network of Parliamentary Budget Offices) da ke gudana a Abuja.

Sarkin Ruman Katsina ya rasu Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja

Abbas ya ƙaryata raɗe-raɗin cewa majalisar ta ƙi amincewa da tsare-tsaren karɓo rance na shugaban ƙasar, inda ya ce zantuka ne marasa tushe da aka ƙirƙira da manufa ta yaudara.

A cewarsa, “kwanan nan, an yi wa jawabin da Shugaban Masu Rinjaye na majalisar ya gabatar a taron majalisun dokoki na Afirka (West African Parliamentary Conference, WAPC) mummunar fassara, har aka rika yi wa majalisar kuskuren fahimta cewar ba ta goyon bayan tsare-tsare da dabarun rancen gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Wannan kuskuren fahimta ne, kuma ba gaskiya ba ce.”

Abbas ya jaddada cewa Majalisar Dokokin Tarayya baki ɗaya, sun amince cewa rance mai tsari cike da kulawa hanya ce da ake amfani da ita wajen gina muhimman ababen more rayuwa, ƙarfafa ci gaban tattalin arziki, da kuma tallafa wa marasa galihu.

Ya bayyana cewa, a ƙarƙashin jagorancin Tinubu, ana karkatar da kuɗaɗen rancen ne zuwa manyan ayyuka da suka haɗa da wutar lantarki, sufuri da noma, waɗanda za su ƙara inganta hanyoyin tattara kuɗaɗen shiga.

Abbas ya kuma tabbatar da cewa duk wani bashi za a karɓo shi ne cikin hikima da kuma tsare-tsaren rance na ƙasar na matsakaicin lokaci da wanda sun dace da duk wasu ƙa’idoji a fadin duniya.

Kazalika, ya jaddada muhimmancin kafa Ofishin Kasafin Kuɗi da Bincike na Majalisa (NABRO) domin yin bincike mai zaman kansa kan batutuwan rance, karɓo bashi da kuma manufofin kuɗi.

Sai dai shugaban majalisar ya yi gargaɗin cewa duk da yake karɓo rancen wajibi ne, amma buƙatar rufe ɓarakar sata da fitar da kuɗaɗen haramun ita ma babban lamari ne da ya zama tilas.

Ya bayyana cewa Najeriya na asarar kusan dala biliyan 18 duk shekara ta hanyar cin hanci da zamba da kuma halasta kuɗaɗen haramun — adadin da ya kai kusan kashi 3.8% na GDP.

Abbas ya ce haɗa rance mai tsari da kuma tsauraran matakan sa ido da yaƙi da cin hanci shi ne zai tabbatar da makomar tattalin arzikin Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Larijani: Donald Trump Yana A Matsayin Makwafin Adolf Hitler
  • Mun ci ribar Naira biliyan 601 a watanni shidan farkon 2025 – Bankin GT
  • CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100
  • Tattalin arzikin Najeriya ya ƙara haɓaka — NBS
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80
  • Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI
  • Trump Ya Bukaci Afganistan Ta Mayarwa Amurka Sansanin Jiragen Sama Na bagram