Leadership News Hausa:
2025-08-09@12:32:03 GMT

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Published: 9th, August 2025 GMT

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Ganawar da shugaba Trump ya yi a baya-bayan nan da shugabannin wasu ƙasashe biyar dake nahiyar Afirka, ita ma ta janyo hankalin al’ummun duniya. Inda shugaba Trump ya yabawa shugaban ƙasar Laberiya Joseph Boakai kan yadda ya iya Turancin Ingilishi sosai, lamarin da ya bayyana rashin fahimtarsa kan alaƙar tarihi tsakanin ƙasar Laberiya da Amurka.

Bugu da ƙari, Trump ya katse maganar shugaban Ƙasar Mauritaniya Mohammed Ghazouani, inda ya nemi ya yi magana da sauri.

A hakika, rashin mutuntawa da shugaba Trump ya nuna a fili, ta bayyana ainihin dalilin da ya sa aka gayyaci shugabannin Afirka biyar zuwa wajen ganawar, ba domin neman ƙarfafa dangantaka ba ne, sai dai don tabbatar wa Amurka ɗin damar samun ma’adanan da take buƙata, da yiwuwar sanya waɗannan ƙasashen dake nahiyar Afirka amincewa da karɓar baƙin haure da ake korarsu daga Amurka.

Wataƙila, shugaba Trump ba ya mai da hankali sosai kan ɗa’a a fannin diflomasiyya, amma idan aka kwatanta da shugabannin ƙasar Amurka da suka gabace shi, to, a ƙalla yana bayyana komai a fili ba tare da rufa-rufa ba.

Maganarsa da matakan da ya ɗauka, dukkansu na isar da saƙo zuwa ga ƙasashen Afirka cewa: “Ba ku cikin jerin fannonin da Amurka take nunawa fifiko.”

“Za mu iya musayar wasu abubuwa, amma kada ku yi tsammanin za ku samu riba ko alfanu sosai.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano

Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Wakilai, Abubakar Kabir Abubakar, ya ce Gwamnatin Tarayya za ta kashe Naira tiriliyan daya da rabi don gina layin dogo na zamani domin saukaka harkar sufuri a cikin birnin Kano.

Ya bayyana hakan ne lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a Kano, inda ya ce aikin zai saukaka wa mazauna birnin wahalar da suke sha a harkar sufuri.

Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano

Ya ce, “Wannan aikin na gina layin dogo na zamani ya kai Dalar Amurka biliyan daya, kwatankwacin Naira tiriliyan daya da rabi.

“Ga wadanda suke tafiye-tafiye zuwa kasashen waje, musamman kasashen Turai da nahiyar Asiya, sun san akwai irin wadannan ayyukan kuma suna da muhimmanci. Aikin zai kara habaka tattalin arzikin jihar idan aka kammala shi.”

Dan majalisar ya kuma ce sabanin yadda ake yadawa, Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya bullo da muhimman ayyukan raya kasa a bangarorin lafiya da aikin gona da ilimi da kuma tsaro a Arewacin Najeriya.

“Abin mamaki ne idan na ji wasu mutane na cewa Shugaba Tinubu bai damu da Arewa ba. Ni ne shugaban kwamitin kasafin kudi, kuma na san me ya yi wa Arewa.

“Ya kamata mu ajiye son rai a gefe guda mu fada wa kanmu gaskiya a kan Shugaba Tinubu. Ya bijiro da ayyuka da dama a Arewa da ya kamata a yaba masa,” in ji Abubakar Bichi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya
  • An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro
  • Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
  • Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano
  • Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan
  • Yadda sabbin takunkuman Trump za su shafi tattalin arziƙin duniya
  • Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • Ministan tsaron Ghana da wasu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • Malaman Jami’o’in Isra’ila Sun Nemi Jamus Ta Tilasta Dakatar Da Yakin Gaza