Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig
Published: 9th, August 2025 GMT
Manchester United sun kammala sayen ɗan wasan gaba na RB Leipzig, Benjamin Sesko, a kan kuɗi kimanin fam £73.7 miliyan. Sesko, ɗan ƙasar Slovenia mai shekaru 22, ya rattaba hannu kan kwangilar shekaru biyar tare da ƙungiyar. An biyan £66.3m kai tsaye, yayin da sauran kuɗin zai kasance a matsayin ƙari (add-ons).
Wannan shi ne sayen ɗan wasa na uku a ɓangaren gaba da United suka yi a wannan kakar, bayan sayen Matheus Cunha a kan fam £62.5m da Bryan Mbeumo a fam £65m, wanda £6m na ƙari ne. Dukansu an gabatar da su ga magoya bayan ƙungiyar kafin wasan wasannin shirin kakar a gida da Fiorentina ranar Asabar.
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran PhilippinesƘungiyoyin da suke neman Sesko sun haɗa da Newcastle United amma ya zaɓi tafiya ƙungiyar Ruben Amorim. United ta kammala kakar wasa ta baya a matsayi ta 15 a Premier League, yayin da Newcastle ta ƙare a matsayi na biyar kuma ta samu shiga gasar Champions League tare da lashe kofin EFL.
Sesko ya bayyana cewa ya na matukar jin daɗin damar da zai samu a Manchester United. Ya ce, “Tarihin Manchester United na da matuƙar muhimmanci, amma abin da ya fi ɗaukar hankalina shi ne makomar ƙungiyar. Daga lokacin da na iso, na ji yanayi mai kyau da kuma haɗin kai na dangi da ƙungiyar ta ƙirƙira.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Hatsarin mota ya yi ajalin mutum 4, 16 sun jikkata a Yobe
Aƙalla mutum ne sun rasu, yayin da wasu 16 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya auku a Ƙaramar Hukumar Karasuwa, a Jihar Yobe.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Yobe, SP Dungus Abdulkareem ne, ya tabbatar da faruwar hatsarin ya faru a ranar Asabar da misalin ƙarfe 2:50 na rana a ƙauyen Zangon Kanwa.
Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro An sanya tukwicin N10m domin kama makasan limamin coci a EnuguHatsarin ya rutsa da mota ƙirar Toyota Hiace wadda ke ɗauke da fasinjoji daga Jakusko zuwa kasuwar Jajimaji da kuma mota ƙirar Volvo daga garin Azare.
Rahoto ya nuna cewa mota ƙirar bas ce ta ƙwace ta buga wani Keke Napep sannan ta ci karo da babbar motar.
Sakamakon haka, direban bas ɗin, Ibrahim Makeri, tare da fasinjoji biyu; Adamu Isiya da Alhaji Shaibu sun rasu nan take.
Daga baya kuma wani daga cikin waɗanda suka ji rauni ya rasu, wanda ya kawo adadin waɗanda suka mutu zuwa huɗu.
An kai gawarwakin da kuma waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Gashuwa da ke Ƙaramar Hukumar Bade.
Likitoci suka tabbatar da mutuwar waɗanda suka rasu, sauran kuwa suna samun kulawa.