Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig
Published: 9th, August 2025 GMT
Manchester United sun kammala sayen ɗan wasan gaba na RB Leipzig, Benjamin Sesko, a kan kuɗi kimanin fam £73.7 miliyan. Sesko, ɗan ƙasar Slovenia mai shekaru 22, ya rattaba hannu kan kwangilar shekaru biyar tare da ƙungiyar. An biyan £66.3m kai tsaye, yayin da sauran kuɗin zai kasance a matsayin ƙari (add-ons).
Wannan shi ne sayen ɗan wasa na uku a ɓangaren gaba da United suka yi a wannan kakar, bayan sayen Matheus Cunha a kan fam £62.5m da Bryan Mbeumo a fam £65m, wanda £6m na ƙari ne. Dukansu an gabatar da su ga magoya bayan ƙungiyar kafin wasan wasannin shirin kakar a gida da Fiorentina ranar Asabar.
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran PhilippinesƘungiyoyin da suke neman Sesko sun haɗa da Newcastle United amma ya zaɓi tafiya ƙungiyar Ruben Amorim. United ta kammala kakar wasa ta baya a matsayi ta 15 a Premier League, yayin da Newcastle ta ƙare a matsayi na biyar kuma ta samu shiga gasar Champions League tare da lashe kofin EFL.
Sesko ya bayyana cewa ya na matukar jin daɗin damar da zai samu a Manchester United. Ya ce, “Tarihin Manchester United na da matuƙar muhimmanci, amma abin da ya fi ɗaukar hankalina shi ne makomar ƙungiyar. Daga lokacin da na iso, na ji yanayi mai kyau da kuma haɗin kai na dangi da ƙungiyar ta ƙirƙira.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Tsohon shugaban jam’iyyar PDP kuma tsohon ministan noma daga 2015 zuwa 2019, Audu Ogbeh, ya rasu a ranar Asabar, 9 ga Agusta, yana da shekaru 78 a duniya, kamar yadda iyalinsa suka tabbatar.
A cikin wata sanarwa, iyalan sun ce: “Ya rasu cikin kwanciyar hankali, ya bar mana gado na gaskiya, hidima da jajircewa ga kasa da al’umma. Mun sami kwanciyar hankali daga yadda ya shafi rayuka da kuma yadda ya kafa misali.”
Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – InuwaIyalan sun bayyana cewa za a sanar da yadda za a gudanar da jana’izarsa a nan gaba, tare da godewa abokai, da abokan aiki. Sun kuma roƙi a basu dama domin yin jimamin rasuwar baban nasu.
Rahoton LEADERSHIP ya nuna cewa Ogbeh, wanda ya shahara a siyasa, rubuce-rubuce da aikin gona, ya shugabanci PDP daga 2001 zuwa 2005 kafin ya zama minista a gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp