Kyari ya ce, a yanzu ana noma Waken Soya da ya kai kimanin tan miliyan 1.35, wanda kuma buƙatar da ake da shi a ƙasar ya wuce tan miliyan 2.7.

Ya sanar da cewa, wanan tsari zai kuma amfani tattalin arziƙin ƙasar da ƙara samar da ayyuakn yi da kuma ƙara haɓaka samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Shi kuwa a nasa jawabin a wajen ƙaddamarwar, Gwamnan Jihar Biniwai, Hyacinth Iormem Alia, ya jaddada muhimmancin da za a amfana da shi a tsarin.

“Dabarun faɗaɗa noman Waken Soya na ƙasa, mataki ne da ya dace wajen yin haɗaka, domin samar da kuɗaɗen shiga ga ƙasar a duk shekara da suka kai kimanin Naira tiriliyan 3.9 da ƙara ƙirƙiro da ayyukan yi a ɗaukacin jihohi 22, ciki har da Abuja, wanda hakan zai kuma ƙara ɗaga martabar Nijeriya a idon duniya a fannin aikin noma”, in ji Hyacinth.

Ya kuma goyi bayan shirin ruɓanya samar da ingantaccen Irin Waken Soya da kuma rabar da shi ga sama da masu nomansa kimanin 200,000, nan da shekara uku masu zuwa.

“Wannan tamkar kira ne na fara gudanar da wani, kuma kira ne ga al’ummominmu da ke karkara da kuma ƙanannan manoma har ga tattalin arziƙin ƙasarmu” a cewar gwamnan.

Ya sanar da cewa, tun lokacin da aka gabatar da samfurin Waken Soya na ‘Malayan’ a shekarar 1937, albarkar ƙasar noma ta Guinea Saɓanna, hakan ya sanya manoma a yankin, ƙara mayar da hankali wajen nomansa, saboda irin dausayin da ƙasar noman ke da shi.

“Ƙasar noma ta Jihar Biniwai, cike take da albarka, wanda hakan ya bai wa jihar damar kasancewa kan gaba wajen noman Waken Soya a Nijeriya da ma Afirka ta Yamma baki-ɗaya,” in ji gwamnan.

Har ila yau, gwamnan ya bayyana cewa; jiharsa na da ƙudurin ruɓanya noman na Waken Soya daga tan 202,000 zuwa aƙalla tan 400,000, nan da shekara uku masu zuwa, wanda hakan zai ba ta damar noma Waken sama da tan 400,000 a duk shekara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Soya beans Wake

এছাড়াও পড়ুন:

An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibai

Majalisar Tarayya ta amince da hukuncin cin sarƙa ga duk wani malami da aka samu da laifin cin zarafi ko lalata da ɗalibai a makarantu a faɗin ƙasar nan.

Hakan ya biyo bayan amincewar majalisar da Dokar Hana Lalata da Dalibai ta 2025 (HB.1597), bayan tsallake karatu na uku a Majalisar Dattawa da kuma Majalisar Wakilai a ranar Laraba.

Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano Jirgin ƙasa ya murƙushe babur mai ƙafa uku a Jos

A ƙunshin bayanan da dokar, za a iya yanke wa duk wanda ya saɓa mata hukuncin ɗaurin shekara 14 ko shekara biyar mafi ƙaranci ba tare da zaɓin biyan tara ba.

Laifukan da dokar ta bayyana a matsayin cin zarafi sun haɗa da yin jima’i ko neman wata alfarma daga ɗalibai a madadin jima’i, barazana, ko tozartarwa da ɗaga hankali a wajen karatu, ko taɓawa ko rungumar jiki.

Haka kuma dokar ta haɗa da aika saƙonnin batsa, hotuna ko bidiyo, ko barkwanci ko magana mai ɗauke da cin zarafi kan jikin ɗalibi, da kuma bibiya da sa ido mai tsanani.

Sabuwar dokar, wadda ke jiran sahalewar shugaban ƙasa kafin ta fara aiki, ta bai wa waɗanda abin ya shafa damar shigar da ƙarar malamin da ya aikata laifin na cin amana.

Haka kuma dokar ta wajabta wa duk makarantu na gaba da sakandare su kafa kwamitin musamman mai zaman kansa domin kula da korafe-korafe da suka shafi cin zarafi, a bisa tsarin doka.

Dokar ta ce ba za a ɗauki yarda daga ɗalibi a matsayin hujja ta kare kai ba, sai idan ɓangarorin biyu sun yi aure bisa doka. Ta kuma bayyana cewa ba sai an tabbatar da niyyar cin zarafi ba kafin a samu hukunci.

Haka zalika, ta haramta wa makarantu gudanar da bincike na cikin gida idan an riga an kai ƙara kotu, inda ta ce har sai an gama shari’ar kafin su iya shiga tsakani.

Dokar ta kuma bai wa ɗalibai, ’yan uwa, wali ko lauya damar kai ƙara, tare da ba da damar miƙa rahoto ga rundunar ‘yan sanda ko ofishin Antoni-Janar, sannan a tura kwafin ƙarar ga kwamitin hana cin zarafi na makarantar da abin ya shafa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
  • An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa
  • An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibai