Kyari ya ce, a yanzu ana noma Waken Soya da ya kai kimanin tan miliyan 1.35, wanda kuma buƙatar da ake da shi a ƙasar ya wuce tan miliyan 2.7.

Ya sanar da cewa, wanan tsari zai kuma amfani tattalin arziƙin ƙasar da ƙara samar da ayyuakn yi da kuma ƙara haɓaka samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Shi kuwa a nasa jawabin a wajen ƙaddamarwar, Gwamnan Jihar Biniwai, Hyacinth Iormem Alia, ya jaddada muhimmancin da za a amfana da shi a tsarin.

“Dabarun faɗaɗa noman Waken Soya na ƙasa, mataki ne da ya dace wajen yin haɗaka, domin samar da kuɗaɗen shiga ga ƙasar a duk shekara da suka kai kimanin Naira tiriliyan 3.9 da ƙara ƙirƙiro da ayyukan yi a ɗaukacin jihohi 22, ciki har da Abuja, wanda hakan zai kuma ƙara ɗaga martabar Nijeriya a idon duniya a fannin aikin noma”, in ji Hyacinth.

Ya kuma goyi bayan shirin ruɓanya samar da ingantaccen Irin Waken Soya da kuma rabar da shi ga sama da masu nomansa kimanin 200,000, nan da shekara uku masu zuwa.

“Wannan tamkar kira ne na fara gudanar da wani, kuma kira ne ga al’ummominmu da ke karkara da kuma ƙanannan manoma har ga tattalin arziƙin ƙasarmu” a cewar gwamnan.

Ya sanar da cewa, tun lokacin da aka gabatar da samfurin Waken Soya na ‘Malayan’ a shekarar 1937, albarkar ƙasar noma ta Guinea Saɓanna, hakan ya sanya manoma a yankin, ƙara mayar da hankali wajen nomansa, saboda irin dausayin da ƙasar noman ke da shi.

“Ƙasar noma ta Jihar Biniwai, cike take da albarka, wanda hakan ya bai wa jihar damar kasancewa kan gaba wajen noman Waken Soya a Nijeriya da ma Afirka ta Yamma baki-ɗaya,” in ji gwamnan.

Har ila yau, gwamnan ya bayyana cewa; jiharsa na da ƙudurin ruɓanya noman na Waken Soya daga tan 202,000 zuwa aƙalla tan 400,000, nan da shekara uku masu zuwa, wanda hakan zai ba ta damar noma Waken sama da tan 400,000 a duk shekara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Soya beans Wake

এছাড়াও পড়ুন:

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Nijeriya ta kasance ƙasa ce, mai girman gaske, wadda kuma ‘yan ta’adda masu iƙirarin jihadi, Al-kamar irinsu; Al- Ƙaeda da ISIS da ke aikata ayyukan ta’addancinsu a yankin Sahel ke kutsowa cikin ƙasar, domin aikata ta’addanci.

Bugu da ƙari, ba tun yau ne, wasu ƙwararru a ɓangaren tsaro na ƙasar nan, suke yin gargaɗin cewa, yadda aka bar iyakokin ƙasar sakakai ne, ke ƙara ta’azzara matsalar tsaro a ƙasa, inda wasu’yan ta’adda daga wajen ƙasar, ke yin amfani da damar, wajen shigowa tare da kuma shigo da muggan makamai da yadda masu ra’ayin riƙau na addini, daga ƙasashe kamar su, Mali da Jamhuriyar Nijar da Chadi, ke shigowa ƙasar, su kuma ci Karensu ba babbaka.

Misali, ‘yan ta’addar ƙungiyar Lakurawa, masu iƙirarin jihadi, waɗanda ta hanyar ayyukan ta’addacin su, suka hana wasu yankuna musamman a Arewa Maso Yamma sakat, daga nan kuma suka ƙara faɗaɗa ta’addacinsu, zuwa wasu yankuna na Arewa Maso Gabas da kuma zuwa iyakokin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar.

Hakazalika, wasu rahotanni sun nuna cewa, ‘yan ta’addar Lakurawan ‘yan aware nada alaka da ƙungiyar masu iƙirarin jihadi da ke gudanar da ayyukansu na ta’addanci, a yankin Sahel, waɗanda shigarwarsu wasu yankuna na Arewa Maso Yammacin ƙasar nan, suka samu damar janyo suke janyo ra’ayoyin wasu matasa cikin ƙungiyar da kuma auren wasu da yankunan na Arewa Maso Yamma.

Shi ma wani tsohon mai magana da yawun rundunar tsaron ƙasar Majo Janar Edward Buba, ya sanar da cewa, ƙungiyar ce, ta ƙara haifar da rudanin siyasa a ƙasashen Mali da Jamhuriyyar Nijar.

Kamar yadda Janar Musa ya faɗa, katange iyakon Nijeriya abu da ke da alfanu da dama ga ƙasar, musamman domin ci gaba da dorewar ƙasar da kuma kare ta, daga hare-hare daga ketare.

Tabbas batun Katange ƙasar, abu ne, da zai laƙumi ɗimbin kuɗaɗe, amma aiwatar da hakan, zai kare Nijeriya daga kutsen ‘yan ta’adda daga wajen aasar.

A wani rahoto da Asusun da ke tallawa kananan yara na majalisar dinkin duniya wato UNICEF, ya yi gargaɗin cewa, rikice-rikicen da ke aukuwa a yankin Sahel ta tsakiya, na kutsawa zuwa wasu ƙasashen da ke maƙwabtaka na yankin, wanda hakan ke kara ta’azzara tarwatsa alumomi daga yankunan su da haifar da matsin tattalin arziki da kuma haifar da  karanci kuɗaɗe.

Duba da yadda iyakokin Nijeriya suke sakakai, wannan matsalar za iya cewa, tamkar kasar, na zaune, a karkashin Bam.

Ya zama wajibi mahukunta a Nijeriya su ɗauki dabaru Nijeriya wajen daƙile shigowar ‘yan ta’adda cikin ƙasar.

Duk da cewar, katange iyakon Nijeriya ba zai hana kutsowar ‘yan ta’adda ba, amma katangewar, za ta taimaka wa hukumomin tsaron ƙasar wajen ƙaukar matakan gaggawa na mayar da martani, ta hanyar yin amfani da kayan aiki na sanya ido.

Tsawon iyakonin Nijeriya, ya kai sama da kilomita 4,000 kilomita, wanda hakan ke nuna cewa, sun fi ƙarfin jami’an hukumar kula da shige da fice, iya kula da iyakokin su kaɗai.

Hakazalika, salon shugabanci a ƙasar na rashin nuna damuwa, ya sanya iyakokin ƙasar sun kasance wajen na samun damar shigowar ɓata gari cikin ƙasar, musamman ga ‘yan ta’addar daga yankin Sahel.

Akwai wasu dabarun zamani da ya kamata a runguma a ƙasa na katange iyakokin ƙasar.

Alamisali, ƙasar Fakistan wadda ta yi iyaka da ƙasar Afghanistan, kusan ta kammala katange iyakokinta masu tsawon kilomita 2,611 wanda aikin ya kai kaso 98.

Kazalika, ƙasar Saudi Arabiya, wadda ta yi iyaka da ƙasar Iraki, ta katange iyakar da ƙasar tsawon kilomita 900 domin daƙile shigowar masu fasakwari da kuma barazanar ‘yan ta’adda.

Wadannan misalan kaɗai, sun isa hujjar da nuna cewa, katange iyakokin ƙasa tare da yin amfani da kayan fasahar zamani, za su taimaka wajen ƙara tabbatar ƙasa. 

Batun gaskiya a nan shi ne, mun yi ammanar cewar cewa, rashin tsaron da ke ci gaba da addabar Nijeriya ba daga cikin gida Nijeriya ba ne, daga ƙetare ne.

A ra’ayin wannan Jaridar, muma muna goyon bayan kiran na  Janar Musa, na buƙatar a katange iyakokin ƙasa, domin kuwa, bai kamata ace, Nijeriya ta yi wani jinkirin aiwatar da hakan ba. Wannan ne matsayar mu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfara 
  • Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
  • ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe
  • PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027
  • Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
  • Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 
  • Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin ministoci ba — Sarki Sanusi II
  • Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin minista ba — Sarki Sanusi II