Aminiya:
2025-11-27@21:56:07 GMT

Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara

Published: 12th, August 2025 GMT

Sojoji sun samu nasarar kai wani gagarumin farmaki kan maboyar ’yan ta’addan da suka addabi manoma da mazauna wasu ƙauyuka a Jihar Zamfara da ke Arewa maso Yammacin Nijeriya.

Bayanai sun ce dakarun sojin na sama da ta ƙasa, waɗanda ke ƙarƙashin rundunar Operation Fasan Yamma da ke sintiri a Arewa maso Yamma domin kawar da masu tayar da ƙayar baya, sun hallaka sama da ’yan ta’adda 400 a yayin wannan samamen.

Za a gyara tarbiyar tubabbun ’yan daban Kano Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya

Majiyoyi sun bayyana cewa ’yan ta’addan, waɗanda ke fakewa a dajin Makakkari tare da shugabanninsu daban-daban, sun dauki haramar kai hari kan wani ƙauye ne kafin sojojin su tari hanzarinsu.

Aminiya ta ruwaito cewa wannan farmakin na zuwa ne bayan zanga-zangar lumana da mazauna birnin Gusau suka gudanar a makon da ya gabata kan yadda matsalar tsaro ta ƙara tsananta a jihar.

Ana iya tuna cewa, a ranar Alhamis da ta gabata ce daruruwan mata, galibi tsofaffi da masu juna biyu daga ƙauyen Jimrawa, Kaura Namoda, suka fito kan titi domin nuna adawa da yadda matsalar rashin tsaron ta tsananta a bayan nan.

Mazauna dai sun yi ƙorafin cewa lalacewar hanyoyi a jihar na taimaka wa ’yan ta’adda wajen kai hare-hare, yayin da jami’an tsaro ke samun matsala wajen isa wuraren da ke fuskantar hare-hare  a kan kari.

Da yake ƙarin haske a ranar Litinin game da farmakin da sojoji suka kai a ranar Lahadi, mai magana da yawun rundunar sojin sama, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya ce bayan samun sahihan bayanan leƙen asiri, an gano kai-komon fiye da ‘yan ta’adda 400 suna shirin kai hari.

Ejodame ya ce: “An yi musu luguden wuta ta sama da ƙasa, inda aka kashe shugabannin ’yan ta’adda da dama da mabiyansu masu yawa.”

Ya ƙara da cewa, “haɗin kan da aka samu tsakanin sojojin sama da na ƙasa ne ya sanya wannan nasarar da muka samu ta zama ta musamman.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Zamfara yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE

Daga Usman Muhammad Zaria 

Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba, ya aiwatar da wani aiki na da naira miliyan biyar domin tallafa wa aiwatar da Shirin Tallafawa Yara Mata  (AGILE) a yankin.

Aikin ya hada da gyaran ajujuwa biyu da samar da muhimman kayan aiki, ciki har da injunan dinki, injin yin surfani wato (monogram) da shirin AGILE ya bayar kyauta wanda Dr. Uba ya shirya, ya taimaka wajen ganin an fara amfani da shi, tare da samar da janareta da tabarmi domin inganta koyarwa da horo.

Wannan ci gaban ya biyo bayan wani bincike da tawagar AGILE ta jihar Jigawa ta gudanar a baya, inda ta bayyana cewa wuraren koyon sana’o’in na bukatar gyara.

Shirin AGILE, wani shiri ne na Gwamnatin Tarayya tare da hadin gwiwar Gwamnatin Jihar Jigawa, wanda aka ƙirƙira domin bai wa matasa mata ƙwarewar da za su dogara da kansu, inda ake sa ran mutum 50 za su amfana a horon da ke tafe.

 

A lokacin ƙaddamar da aikin, Mai kula da shirin AGILE a Birnin Kudu, Hajiya Maryam Hassan Jibrin, ta yaba da jajircewar Dr. Builder Uba ga ci gaban al’umma, tana jinjinawa kokarinsa tare da yi masa addu’ar ci gaba da jagoranci mai tasiri.

Da yake tabbatar da jajircewar gwamnatinsa wajen ci gaban matasa, Muhammad Uba ya yi alƙawarin bayar da gagarumin tallafi ga mahalarta bayan kammala shirin cikin nasara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina