Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
Published: 12th, August 2025 GMT
Sojoji sun samu nasarar kai wani gagarumin farmaki kan maboyar ’yan ta’addan da suka addabi manoma da mazauna wasu ƙauyuka a Jihar Zamfara da ke Arewa maso Yammacin Nijeriya.
Bayanai sun ce dakarun sojin na sama da ta ƙasa, waɗanda ke ƙarƙashin rundunar Operation Fasan Yamma da ke sintiri a Arewa maso Yamma domin kawar da masu tayar da ƙayar baya, sun hallaka sama da ’yan ta’adda 400 a yayin wannan samamen.
Majiyoyi sun bayyana cewa ’yan ta’addan, waɗanda ke fakewa a dajin Makakkari tare da shugabanninsu daban-daban, sun dauki haramar kai hari kan wani ƙauye ne kafin sojojin su tari hanzarinsu.
Aminiya ta ruwaito cewa wannan farmakin na zuwa ne bayan zanga-zangar lumana da mazauna birnin Gusau suka gudanar a makon da ya gabata kan yadda matsalar tsaro ta ƙara tsananta a jihar.
Ana iya tuna cewa, a ranar Alhamis da ta gabata ce daruruwan mata, galibi tsofaffi da masu juna biyu daga ƙauyen Jimrawa, Kaura Namoda, suka fito kan titi domin nuna adawa da yadda matsalar rashin tsaron ta tsananta a bayan nan.
Mazauna dai sun yi ƙorafin cewa lalacewar hanyoyi a jihar na taimaka wa ’yan ta’adda wajen kai hare-hare, yayin da jami’an tsaro ke samun matsala wajen isa wuraren da ke fuskantar hare-hare a kan kari.
Da yake ƙarin haske a ranar Litinin game da farmakin da sojoji suka kai a ranar Lahadi, mai magana da yawun rundunar sojin sama, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya ce bayan samun sahihan bayanan leƙen asiri, an gano kai-komon fiye da ‘yan ta’adda 400 suna shirin kai hari.
Ejodame ya ce: “An yi musu luguden wuta ta sama da ƙasa, inda aka kashe shugabannin ’yan ta’adda da dama da mabiyansu masu yawa.”
Ya ƙara da cewa, “haɗin kan da aka samu tsakanin sojojin sama da na ƙasa ne ya sanya wannan nasarar da muka samu ta zama ta musamman.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Zamfara yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
A Mali An Kama Sojoji Fiye da 40 Saboda Zargi da Kokarin Juyin Mulki
Sojojin Kasar Mali kimani 45 aka kama biyu daga cikinsu masu mukamin Janar a karshen makon da ya gabata a kokarin da suka yi na juyin mulki a kasar
Shafin yanar gizo na labarai ;Afrika News: ya bayyana cewa daga cikin wadanda aka kama har da janar Abass Dembele, kuma tsohon gwamna na lardin Tsakiyar Mopti. Majiyoyi kusa da Abbas sun bayyana cewa sojoji sun kama shi ne a safiyar ranar lahadi a wajen birnin Bamako babban birnin kasar, ba tare da wani karin bayani ba.
Har’ila yau labarin ya kara da cewa, Nema Sagara, mai mukaman brigadier General a sojojin sama na kasar, kuma mace wacce ba wanda ya fita mukami a sojojin kasar tana daga cikin wadanda aka kama.
Firai ministan kasar ya bayyana cewa dukkan wadanda aka kama sojoji ne a kasar .Tun watan Augustan shekara 2020 ne kanar Assimi Goita ya jagoranci juyin mulki a mali wanda ya kawo karshen democeadiyya a kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Larijani Ya Gana Da Firai ministan Kasar Iraki A Bagdaza August 11, 2025 Mafi yawan Kasashen Duniya Sun Amince Da Samarda Kasar Falasdinu August 11, 2025 Mahukuntan Iraki Sun Bayyana Cewa: Akwai Yiwuwar Masu Ziyarar Arba’een Na Imam Husaini {a.s} Zasu Zarce Miliyan 4 August 11, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza August 11, 2025 Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar ‘Yan Sahayoniyya Kan Gaza August 11, 2025 Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza August 11, 2025 Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Harin Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza August 11, 2025 Iran: Ba a yanke wani abu game da tattaunawa da Washington ba August 11, 2025 Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza August 11, 2025 Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari August 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci