Aminiya:
2025-10-13@17:12:15 GMT

Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara

Published: 12th, August 2025 GMT

Sojoji sun samu nasarar kai wani gagarumin farmaki kan maboyar ’yan ta’addan da suka addabi manoma da mazauna wasu ƙauyuka a Jihar Zamfara da ke Arewa maso Yammacin Nijeriya.

Bayanai sun ce dakarun sojin na sama da ta ƙasa, waɗanda ke ƙarƙashin rundunar Operation Fasan Yamma da ke sintiri a Arewa maso Yamma domin kawar da masu tayar da ƙayar baya, sun hallaka sama da ’yan ta’adda 400 a yayin wannan samamen.

Za a gyara tarbiyar tubabbun ’yan daban Kano Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya

Majiyoyi sun bayyana cewa ’yan ta’addan, waɗanda ke fakewa a dajin Makakkari tare da shugabanninsu daban-daban, sun dauki haramar kai hari kan wani ƙauye ne kafin sojojin su tari hanzarinsu.

Aminiya ta ruwaito cewa wannan farmakin na zuwa ne bayan zanga-zangar lumana da mazauna birnin Gusau suka gudanar a makon da ya gabata kan yadda matsalar tsaro ta ƙara tsananta a jihar.

Ana iya tuna cewa, a ranar Alhamis da ta gabata ce daruruwan mata, galibi tsofaffi da masu juna biyu daga ƙauyen Jimrawa, Kaura Namoda, suka fito kan titi domin nuna adawa da yadda matsalar rashin tsaron ta tsananta a bayan nan.

Mazauna dai sun yi ƙorafin cewa lalacewar hanyoyi a jihar na taimaka wa ’yan ta’adda wajen kai hare-hare, yayin da jami’an tsaro ke samun matsala wajen isa wuraren da ke fuskantar hare-hare  a kan kari.

Da yake ƙarin haske a ranar Litinin game da farmakin da sojoji suka kai a ranar Lahadi, mai magana da yawun rundunar sojin sama, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya ce bayan samun sahihan bayanan leƙen asiri, an gano kai-komon fiye da ‘yan ta’adda 400 suna shirin kai hari.

Ejodame ya ce: “An yi musu luguden wuta ta sama da ƙasa, inda aka kashe shugabannin ’yan ta’adda da dama da mabiyansu masu yawa.”

Ya ƙara da cewa, “haɗin kan da aka samu tsakanin sojojin sama da na ƙasa ne ya sanya wannan nasarar da muka samu ta zama ta musamman.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Zamfara yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja

Wani soja mai muƙamin Las Kofur ya ɗirka wa matarsa harbi har lahira sannan ya kashe kansa a Jihar Neja.

Las Kofur Akenleye Femi da ke aiki a Bataliya ta 221, ya yi wannan aika-aika ne a Barikin Sojoji na Wawa da ke Ƙaramar Hukumar Borgu a Jihar Neja.

Muƙaddashin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Soja ta 22 da ke Ilorin, Kyaftin Stephen Nwankwo, ne ya tabbatar da lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce abin ya faru ne a ranar 11 ga Oktoba, 2025.

Ya ce mutuwar sojan da matarsa ta haifar da tashin hankali a cikin sansanin soja, inda mazauna wurin suka shiga ɗimuwa da mamaki kan abin da zai iya jawo irin wannan lamari.

Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako

“An gano gawar Last Kofur Femi da matarsa ne a cikin dakinsu da ke Block 15, Room 24 na Corporals and Below Quarters a Wawa Cantonment,” in ji Kyaftin Nwankwo.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa sojan yana kan aiki a cikin sansanin kafin ya nemi izinin zuwa gida domin wasu bukatun kansa, sai daga bisani aka gano gawarsu a gida.

Kyaftin Nwankwo ya ce an ajiye gawar mamatan domin ci gaba da bincike, kuma rundunar sojan na aiki tukuru don gano musabbabin lamarin.

Rundunar Soja ta Najeriya ta bayyana matuƙar baƙin cikinta kan wannan abin takaici, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalai, abokai da abokan aikin mamatan.

Kwamandan Rundunar, Birgediya Janar Ezra Barkins, ya sha alwashin gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar abin da ya faru, tare da ɗaukar matakan da za su hana faruwar irin haka a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • ’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi 
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara