“Na taɓa zama abar kwatance, musamman a ɓangaren da shafi kuɗi, suna, girmamawa, amma kuskuren da na yi ya zama dalilin da yasa masana’antar ta juya min baya, sakamakon babu abin da na iya ko na sani face; harkar ta fim. Halin da ake ciki yanzu, babu wani tallafi, babu aikin yi, akwai lokacin da ina da ɗimbin masoya da suke son aurena da kuma nuna min soyayya, amma sai na kasa zaɓen wanda zan ci gaba da rayuwata da shi a wancan lokaci.

Babban dalilin da ya jawo min koma-baya a harkar fim shi ne, hatsarin da na samu na mota, wanda Allah ya jarrabce ni da shi, na yi hatsarin mota da har sai da na samu karaya huɗu a ƙafata, sannan kuma na samu buguwa a kaina da har sai da na manta da komai na rayuwa da na sani a wancan lokaci, bugu da gari; fuskata ta samu raunuka masu yawa da suka canza mani fasalin fuskar tawa, hakan ya sa na ɗauki tsawon lokaci ina jinya.

Da ta ke amsa tambaya a kan ko ‘yan’uwan sana’arta na Kannywood sun taimaka mata a lokacin da take cikin wannan mawuyacin hali? Ummi ta ce, duk da babu wani wanda ya ɗauki nauyin jinyarta a wancan lokaci, amma dai ba za ta taɓa mantawa da yadda suka riƙa zuwa har gida suna gaishe ta ba, “Ni na ɗauki nauyin jinyar kaina, saboda bakin gwargwado ina da abin da zan iya ɗaukar nauyin jinyata”, in ji Ummi.

Dangane da da-na-sanin da ta ke yi a rayuwa kuma, Ummi ta ce; babu wani abu da take da-na-sanin rashin yi da ya wuce aure, domin da a ce ta yi aure, zuwa yanzu wataƙila da Allah ya azurta ta da samun zuri’a, waɗanda za su riƙa kula da ita yanzu da kuma bayan ta tsufa. “Don haka, ina fatan yin aure kafin rayuwata ta zo ƙarshe”.

Daga ƙarshe, tsohuwar jarumar ta buƙaci matasa masu tasowa a masana’antar Kannywood, da kada su maimaita irin kuskuren da da yawa daga cikin tsoffin jarumai mata suka yi, “Ina shawartar duka wata mace mai lokaci a masana’antar Kannywood yanzu, da ta tabbatar da cewa; ta saka hannun jari a wasu wuraren kasuwanci da za su riƙa samar mata da wani abu ta yadda ko da lokacin ɗaukakarta ya wuce, za ta ci gaba da yi; domin kula da rayuwarta.

Dalili kuwa shi ne, duk irin ɗaukakar da kika samu a yanzu, lokaci na nan zuwa da dole zai gushe, ki zama kamar ba ki taɓa samun wannan ɗaukaka ba, kamar yadda yanzu ake yi babu mu, duk kuwa da irin shaharar da muka samu a lokutan baya.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kannywood

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu

Shugaba Bola Tinubu ya aike da sunan mutum uku zuwa Majalisar Dattawa, domin tantance su a matsayin sabbin jakadan Najeriya.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne, ya sanar da haka a zaman majalisar na ranar Laraba.

Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna

Waɗanda aka zaɓa su haɗa da Kayode Are daga Jihar Ogun, Aminu Dalhatu daga Jihar Jigawa da kuma Ayodele Oke.

Bayan karanta takardar Tinubu, Akpabio ya ce, “Sunaye uku ne zuwa yanzu, tabbas sauran za su biyo baya.”

Tun bayan ɗarewarsa kan mulki a 2023, Tinubu bai naɗa jakadu ba har yanzu.

Mutane da dama sun daɗe suna ƙorafin kan jinkirin naɗa jakadun.

Amma wasu na ganin aike sunayen jakadun na da alaƙa da barazanar da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na ɗaukar matakin soji a kan Najeriya, kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

A wata hira da aka yi da shi a watan Satumba, Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, ya ce babu wata matsala game da jinkirin.

Ya ce, “Dukkanin ofisoshin jakadancinmu suna aiki yadda ya kamata. Kowace ofishi yana gudanar da ayyukansa yadda ya dace. Rashin jakadu ba zai haifar da giɓi ba.”

Ya ƙara da cewa duk da cewa jakada shi ne shugaban ofishin jakadanci, akwai kwamishinoni, wakilai da ma’aikatan diflomasiyya da ke tafiyar da harkokin yau da kullum.

A cewarsa, “Diflomasiyya ba aikin mutum ɗaya ba ne. Tsarin ya tanadi irin wannan yanayi.”

Tuggar, ya kuma ce shugaban ƙasa ne kaɗai ke da ikon naɗa jakadu, kuma zai yi hakan a lokacin da ya dace.

Ya bayyana cewa, “Shugaban ƙasa yana duba batun, kuma za a sanar da sunayen a lokacin da ya dace.”

Ya ƙara da cewa, “’Yan Najeriya a ƙasashen waje har yanzu suna samun ayyuka, kuma mu’amala da ƙasashen da muke hulɗa da su ba ta ragu ba.”

Ya ce kuma akwai ƙasashe da dama da suka shafe dogon lokaci ba tare da jakadu ba, amma hakan bai lalata dangantakarsu da wasu ƙasashe ba.

Ya ce, “Wannan ba sabon abu ba ne. Diflomasiyya tana da tanadin irin wannan yanayi. Abin da ya fi muhimmanci shi ne aiki, ba kwaikwayo ba.”

A ƙarshe ya ce Najeriya tana aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran ƙasashen duniya.

“Manufofin ƙasashen waje na Najeriya sun bayyana, kuma ana jinmu a duniya. Abin da muke yi shi ne tabbatar da cewa ofisoshinmu suna samar da sakamako mai amfani ga ’yan Najeriya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Na Barazanar Sake Shiga Wani Sabon Yaki Da Kasar Lebanon
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • ’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa