Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Zama Sakatariyar Kungiyar Yaƙi Da Cutar Daji

“Ta hanyar gudanar da ɗimbin ayyukan noma a Gandun Dazukan wannan ƙasa, zai yi matuƙar ƙara yawan ayyukan masana’antun ƙasar da ke sarrafa amfanin gona domin fitarwa zuwa kasuwannin duniya, don sayarwa”, in ji Ibrahim.

Kazalika, Ibrahim wanda kuma shi ne shugaban ƙungiyar manoma ta ƙasa (AFAN) ya jaddada cewa; idan aka samu goyon bayan ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci da kuma goyon bayan sauran hukumomin, hakan zai bayar da damar gyara Gandun Dazukan da ake da su, musamman wajen kare su daga kwararowar hamada.

Shugaban ya ƙara da cewa, akasarin noman gargajiya a ƙasar nan, ana yin sa ne a karkara, inda manoma a karkara ke shuka ‘ya’yan itatuwa na kayan marmari a Gandun Dazukan ƙasar.

Ya ci gaba da cewa, mazauna karkara na yin amfani da Gandun Dazukan ƙasar wajen yin kiwon dabbobi, wanda hakan ke ƙara bunƙasa ayyuka a tsakanin mazauna karkarar.

Shugaban ya yi nuni da cewa, gudanar da ayyukan noma a Gandun Dazukan wannan ƙasa, zai yi matuƙar kawo ci gaba ga Nijeriya tare da samar da ɗauki ga marasa ƙarfi, wanda kuma hakan zai bai wa mata da matasa damar jawo su a jiki, domin tafiya tare da su.

A cewarsa, har yanzu ba a makara ba, domin kuwa za a iya yin amfani da Gandun Dazukan ƙasar wajen gudanar da ayyukan noma.

Shugaban ya ci gaba da cewa, hakan zai ƙara taimaka wa a samar da wadataccen abinci a ƙasar da kare kwararowar hamada da kuma annobar sauyin yanayi.

Ya bayyana cewa, za a iya cimma hakan ne kaɗai idan mahukunta a ƙasar suka samar da kyakywan tsari tare da gangamin wayar da kan jama’a da kuma zuba hannun jari

a fannin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Fish farming

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini

Gwamnatin Tarayya ta yi watsi da matakin da Gwamnatin Amurka ta dauka na sanya sunan Najeriya cikin jerin “Kasashen Da Ake Tauye ’Yancin Addini” , wato jerin kasashen da ake zargi da take hakkin addini.

Ministan Yada Labarai da Al’adu, Mohammed Idris Malagi ne, ya bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja, inda ya ce matsalar tsaro da ake fuskanta a Najeriya ba ta shafi wani rukuni na addini ko kabila kai-tsaye ba.

Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai

Ya ce masu yada bayanan karya ne suka sa ake ganin kamar Najeriya tana nuna bambanci ta fuskar addini.

Malagi, ya ce gwamnati tana ci gaba da kokari wajen inganta harkar tsaro, sai dai ya bayyana cewa jami’an tsaro na wahala wajen isa wasu yankuna masu nisa a kan lokaci, don kai dauki.

Ya kara da cewa gwamnati na shirin dawo da tsarin tsaron al’umma domin tallafa wa rundunar tsaro ta kasa.

Da aka tambaye shi ko rashin nada jakadu ne ya haddasa wannan ce-ce-ku-ce da Amurka, Malagi ya ce dangantakar Najeriya da Amurka da sauran kasashe na tafiya daidai, kuma Shugaba Bola Tinubu na kokarin warware batun nada jakadu.

’Yan siyasar da suka fadi zabe ne ke yada labaran karya — Alake

A nasa bangaren, Ministan Harkokin Ma’adanai, Dele Alake, ya ce wasu ’yan siyasa da suka fadi a zabe ne ke yada labaran karya a Amurka cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya.

Ya gargade su da cewa irin wadannan maganganu na iya haddasa karin tashin hankali wanda zai iya shafar kowa, ba tare da la’akari da addini ba.

Keyamo ya karyata zargin

Shi ma Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya ce ikirarin Amurka karya ne, domin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ba ta nuna wariyar addini.

Ya bayyana cewa yawancin manyan hafsoshin tsaro a Najeriya Kiristoci ne, sannan kuma Tinubu Musulmi ne matarsa Kirista, wacce malamar coci ce.

Keyamo, ya kara da cewa matsalolin tsaro a Najeriya suna shafar Musulmi da Kiristoci baki daya, don haka ya roki gwamnatin Amurka ta taimaka wajen yaki da ta’addanci maimakon dogaro da rahotannin karya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu!
  • Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Najeriya: Ta Sake Jaddada Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka