Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Zama Sakatariyar Kungiyar Yaƙi Da Cutar Daji

“Ta hanyar gudanar da ɗimbin ayyukan noma a Gandun Dazukan wannan ƙasa, zai yi matuƙar ƙara yawan ayyukan masana’antun ƙasar da ke sarrafa amfanin gona domin fitarwa zuwa kasuwannin duniya, don sayarwa”, in ji Ibrahim.

Kazalika, Ibrahim wanda kuma shi ne shugaban ƙungiyar manoma ta ƙasa (AFAN) ya jaddada cewa; idan aka samu goyon bayan ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci da kuma goyon bayan sauran hukumomin, hakan zai bayar da damar gyara Gandun Dazukan da ake da su, musamman wajen kare su daga kwararowar hamada.

Shugaban ya ƙara da cewa, akasarin noman gargajiya a ƙasar nan, ana yin sa ne a karkara, inda manoma a karkara ke shuka ‘ya’yan itatuwa na kayan marmari a Gandun Dazukan ƙasar.

Ya ci gaba da cewa, mazauna karkara na yin amfani da Gandun Dazukan ƙasar wajen yin kiwon dabbobi, wanda hakan ke ƙara bunƙasa ayyuka a tsakanin mazauna karkarar.

Shugaban ya yi nuni da cewa, gudanar da ayyukan noma a Gandun Dazukan wannan ƙasa, zai yi matuƙar kawo ci gaba ga Nijeriya tare da samar da ɗauki ga marasa ƙarfi, wanda kuma hakan zai bai wa mata da matasa damar jawo su a jiki, domin tafiya tare da su.

A cewarsa, har yanzu ba a makara ba, domin kuwa za a iya yin amfani da Gandun Dazukan ƙasar wajen gudanar da ayyukan noma.

Shugaban ya ci gaba da cewa, hakan zai ƙara taimaka wa a samar da wadataccen abinci a ƙasar da kare kwararowar hamada da kuma annobar sauyin yanayi.

Ya bayyana cewa, za a iya cimma hakan ne kaɗai idan mahukunta a ƙasar suka samar da kyakywan tsari tare da gangamin wayar da kan jama’a da kuma zuba hannun jari

a fannin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Fish farming

এছাড়াও পড়ুন:

Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri

Tsohon Ministan Harkokin ’Yan Sanda, Adamu Maina Waziri, ya caccaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu da cewa gwamnatinsa ta kere ta tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta fuskar muni, wanda a yanzu ƙasar tana cikin mummunan bala’i. 

Waziri, wanda jigo ne a jam’iyyar ADC (African Democratic Congress), ya bayyana haka ne a yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talabijin na Trust TV.

’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa

“Babu ta inda gwamnatin Tinubu ba ta gaza ba. Ta gaza a dukkan fannoni, kama daga kan tsaro, tattalin arziki, yaƙi da cin hanci saboda komai ya tabarbare. Nijeriya ta koma baya sosai a ƙarƙashin mulkinsa,” in ji shi.

Duk da ya amince an tafka kura-kurai a gwamnatin Buhari, Waziri ya ce a ganinsa Tinubu ya yi wa tsohon shugaban ƙasar fintinkau ta fuskar gazawa.

Tsohon Ministan ya bayyana cewa mulkin shugaba Tinubu ya jefa ’yan Nijeriya cikin ƙuncin rayuwa, musamman tun bayan janye tallafin mai da sauye-sauyen tattalin arziki, wanda ya janyo hauhawar farashin kaya da ƙarancin abinci.

Ya kuma soki yadda wasu ’yan siyasa ke nuna goyon baya ga gwamnatin Tinubu saboda saboda son zuciya da wani ra’ayi na ƙashin kai, yana mai cewa “wadannan mutanen su kansu suna cikin tsaka mai wuya, amma sai su riƙa yabon gwamnati saboda siyasa.”

Ya ce yana mamakin irin waɗannan mutane musamman waɗanda yankunansu ke fama da hare-haren ’yan bindiga da rashin tsaro za su riƙa fitowa a kafafen watsa labarai suna goyon bayan gwamnati, lamarin da ya bayyana a matsayin mai ɗaure kai.

“Ina mamakin yadda wasu mutane waɗanda ƙananan hukumominsu ke ƙarƙashin ikon ’yan bindiga za su iya fitowa a talabijin na ƙasa su na yabon wannan gwamnati,” in ji shi.

Waziri ya ƙara da cewa, a yanzu Nijeriya na buƙatar shugabanci nagari, wanda babu makirci da ruɗu a cikinsa, saboda haka babu wata gwamnati da ta rasa ƙima irin wannan da za ta nemi wa’adi na biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 
  • Al’ummar Zamfara: ’Yan bindiga sun karɓi N56m domin izinin yin noma
  • NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • Gwamnatin Kwara Ta Horar Da Manoma Sama Da 500 Tare Da Basu Tallafi
  • Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
  • Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
  • Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025
  • Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri