Jarumar Kannywood Rahama Sadau ta yi aure
Published: 9th, August 2025 GMT
Fitacciyar jarumar Kannywood, Rahama Sadau, ta yi aure da masoyinta, Ibrahim Garba.
An ɗaura auren a ranar Asabar a Masallacin da ke Unguwan Rimi, a Jihar Kaduna, bayan Ibrahim ya biya sadaki Naira 300,000.
Za a biya ma’aikata 445 garatutin sama da biliyan ɗaya a Kebbi Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfaraRahama, ta sanar da ɗaurin auren a shafinta na Facebook, inda ta gode wa Allah tare da neman addu’a daga masoyanta.
Ta bayyana farin ciki da godiyarta, tare da fatan wannan sabon babi na rayuwarta zai kasance mai albarka.
Auren mata na zuwa ne watanni biyu bayan rasuwar mahaifinta, Ibrahim Sadau.
’Yan uwanta sun yaɗa hotuna da bidiyon bikin a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama suka yi mamakin yadda aka yi bikin ba tare da sanin jama’a ba.
Rahama, wacce furodusa ce a Kannywood, an naɗa ta memba a Kwamitin Fasaha na shirin Investment in Digital and Creative Enterprise (iDICE).
An ba ta muƙamin ne a 2024 ƙarƙashin ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jaruma kannywood Rahama Sadau
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp