Aminiya:
2025-08-09@19:38:56 GMT

Jarumar Kannywood Rahama Sadau ta yi aure

Published: 9th, August 2025 GMT

Fitacciyar jarumar Kannywood, Rahama Sadau, ta yi aure da masoyinta, Ibrahim Garba.

An ɗaura auren a ranar Asabar a Masallacin da ke Unguwan Rimi, a Jihar Kaduna, bayan Ibrahim ya biya sadaki Naira 300,000.

Za a biya ma’aikata 445 garatutin sama da biliyan ɗaya a Kebbi Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfara 

Rahama, ta sanar da ɗaurin auren a shafinta na Facebook, inda ta gode wa Allah tare da neman addu’a daga masoyanta.

Ta bayyana farin ciki da godiyarta, tare da fatan wannan sabon babi na rayuwarta zai kasance mai albarka.

Auren mata na zuwa ne watanni biyu bayan rasuwar mahaifinta, Ibrahim Sadau.

’Yan uwanta sun yaɗa hotuna da bidiyon bikin a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama suka yi mamakin yadda aka yi bikin ba tare da sanin jama’a ba.

Rahama, wacce furodusa ce a Kannywood, an naɗa ta memba a Kwamitin Fasaha na shirin Investment in Digital and Creative Enterprise (iDICE).

An ba ta muƙamin ne a 2024 ƙarƙashin ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jaruma kannywood Rahama Sadau

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
  • Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfara 
  • Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
  • Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa
  • Obi ya ziyarci Bauchi, ya ba da tallafin N15m don inganta ilimi
  • Majalisar Jigawa Ta Yi Karatu Na Biyu Kan Dokar Fansho Ga Tsofaffin Shugabanni
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara
  • An Biya Diyyar Naira Miliyan 277 Ga Wadanda Aikin Ginin Masallacin Gumel Ya Shafa
  • Ana zargin ‘yan sandan da karya hannun Sawore