Aminiya:
2025-10-13@17:12:46 GMT

Hukumar Kwatsam ta kama makamai da ƙwayoyin N10bn a Legas

Published: 12th, August 2025 GMT

Hukumar Kwastam Najeriya ta kama kwantainoni 16 ɗauke da makamai da miyagun ƙwayoyi da magungunan da wa’adin aikinsu ya ƙare da wasu haramtattun kaya na kimanin Naira 10 a Tashar Jiragen Ruwa ta Apapa da ke Jihar Legas a ranar Litinin.

Hukumar ta bayyana cewa ta kama mutane shida dangane da wannan haramtattun kaya da aka yi fasa-ƙwaurin su zuwa Najeriya.

Kwanturola Janar na Kwastam, Adewale Adeniyi, ya sanar da cewa an yi ƙarya wajen bayyana kayan da  kwantainonin suke ɗauke da su, inda aka ɓoye makamai, harsasai da magungunan da ba su da rajista.

“A yau, muna sanar da kama kwantainoni 16 da shigowarsu ke karya dokokinmu kuma suna barazana ga tsaron ƙasa. Darajar harajin da za a biya kan waɗannan kaya ya haura Naira biliyan 10,” in ji Shugaban Hukumar.

Yadda ɗan shekara 70 ya rasu a gobarar tankokin gas a Zariya EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato Aminu Tambuwal kan zargin N189bn

Kayan da aka kama sun haɗa da:

– Bindigogi biyu na pump-action, bindiga ɗaya nau’in Smith & Wesson da harsasai fiye da 80

– Kwalaye 202 na kayan maye (Colorado Loud), nauyinsu ya kai kilo 101

– Kwantainoni 7 na magungunan da suka daina da haramtattu

– Kwantainoni 3 na abinci da ya lalace.

– Kwantainoni 3 na haramtattun tufafi

– Kwantainoni 2 ɗauke da magungunan codeine

– Kwantaina ɗaya da ke ɗauke da kwalaye 305 na man goge baki na ƙarya da aka ɓoye da ɗinki da kayan ado

Adeniyi ya ce an gudanar da binciken tare da haɗin gwiwar Hukumar NDLEA da sauran hukumomin gwamnati.

Ya jaddada cewa har yanzu an dakatar da amfani da tashoshin wajen fitar da magunguna.

An kama mutane biyar, inda uku daga cikinsu aka gurfanar da su kuma suna tsare a gidan yari na Ikoyi har sai an fara shari’ar su.

Hukumar Kwastam ta ce tana aiki da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa don gano tushen waɗannan kaya da hana Najeriya zama wurin zubar da haramtattun kaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwastam ƙwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya October 13, 2025 Manyan Labarai Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako October 13, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Tarihin Hassan Usman Katsina (1)
  • A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano