Hukumar Kwatsam ta kama makamai da ƙwayoyin N10bn a Legas
Published: 12th, August 2025 GMT
Hukumar Kwastam Najeriya ta kama kwantainoni 16 ɗauke da makamai da miyagun ƙwayoyi da magungunan da wa’adin aikinsu ya ƙare da wasu haramtattun kaya na kimanin Naira 10 a Tashar Jiragen Ruwa ta Apapa da ke Jihar Legas a ranar Litinin.
Hukumar ta bayyana cewa ta kama mutane shida dangane da wannan haramtattun kaya da aka yi fasa-ƙwaurin su zuwa Najeriya.
Kwanturola Janar na Kwastam, Adewale Adeniyi, ya sanar da cewa an yi ƙarya wajen bayyana kayan da kwantainonin suke ɗauke da su, inda aka ɓoye makamai, harsasai da magungunan da ba su da rajista.
“A yau, muna sanar da kama kwantainoni 16 da shigowarsu ke karya dokokinmu kuma suna barazana ga tsaron ƙasa. Darajar harajin da za a biya kan waɗannan kaya ya haura Naira biliyan 10,” in ji Shugaban Hukumar.
Yadda ɗan shekara 70 ya rasu a gobarar tankokin gas a Zariya EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato Aminu Tambuwal kan zargin N189bnKayan da aka kama sun haɗa da:
– Bindigogi biyu na pump-action, bindiga ɗaya nau’in Smith & Wesson da harsasai fiye da 80
– Kwalaye 202 na kayan maye (Colorado Loud), nauyinsu ya kai kilo 101
– Kwantainoni 7 na magungunan da suka daina da haramtattu
– Kwantainoni 3 na abinci da ya lalace.
– Kwantainoni 3 na haramtattun tufafi
– Kwantainoni 2 ɗauke da magungunan codeine
– Kwantaina ɗaya da ke ɗauke da kwalaye 305 na man goge baki na ƙarya da aka ɓoye da ɗinki da kayan ado
Adeniyi ya ce an gudanar da binciken tare da haɗin gwiwar Hukumar NDLEA da sauran hukumomin gwamnati.
Ya jaddada cewa har yanzu an dakatar da amfani da tashoshin wajen fitar da magunguna.
An kama mutane biyar, inda uku daga cikinsu aka gurfanar da su kuma suna tsare a gidan yari na Ikoyi har sai an fara shari’ar su.
Hukumar Kwastam ta ce tana aiki da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa don gano tushen waɗannan kaya da hana Najeriya zama wurin zubar da haramtattun kaya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargin ’yan kungiyar asiri ne tare da kwato musu wasu abubuwa na bata gari a Ilorin.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, Adetoun Ejinre-Adeyemi ya fitar, ya ce, ‘yan sandan da ke aiki bisa sahihiyar bayanan sirri daga majiyoyin tsaron al’umma, sun dauki wami mataki kan wani harin fashi da makami da ya afku a wani dakin kwanan dalibai da ke unguwar Eleko, Ilorin.
Sanarwar ta ce ba tare da bata lokaci ba jami’an ‘yan sanda da ‘yan banga, sun kai ga kama wasu maza biyu da ake zargi.
Ta ce wadanda ake zargin sun hada da Ishola Adeyemi, da Ismail Rafiu dukkansu na Ibadan, jihar Oyo.
A cewarsa yayin da ake yi musu tambayoyi na farko, wadanda ake zargin sun amsa cewa wani Qudus mai suna “Tiny”, memba ne na kungiyar Ido Cult Fraternity, ya gayyace su zuwa Ilorin don kawar da wani dan kungiyar asiri.
Ya yi nuni da cewa, a lokacin da harin nasu bai yi nasara ba, sai suka koma yin fashi a gidajen kwanan dalibai a yankin.
Ya yi bayanin cewa wadanda ake zargin, tare da baje kolin da aka kwato an mika su zuwa Sashen Yaki da Fashi, Sashen Binciken Laifukan Jiha (SCID), hedikwatar Jiha, don ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a gaban kotu.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU