Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza
Published: 11th, August 2025 GMT
Sojojin mamayar Isra’ila sun harba wata mugunyar ‘karfin wuta’ da jiragen saman yaki kan yankin kudancin Gaza
Bayan tsakar dare ne jiragen yakin sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kaddamar da luguden wuta a kudancin birnin Gaza.
Cibiyar yada labaran Falasdinu ta nakalto majiyoyin da ta bayyana a matsayin na cikin gida na cewa: Jiragen saman sojin mamayar Isra’ila sun kaddamar da hare-haren wuce gona da iri, inda suka harba makamai masu linzami sama da 20 cikin ‘yan mintuna a kudancin mahadar Al-Musalaba da Dawla da kuma kusa da masallacin Ali, inda suka nufi kudu.
Wakilin cibiyar ya ruwaito cewa, galibin hare-haren sun fi karkata ne a kan titin 8 da ke kudancin Gaza.
Wadannan hare-haren dai na zuwa ne a daidai lokacin da barazanar da sojojin mamaya ke yi na kaddamar da wani gagarumin farmaki a kan birnin na Gaza ke kara ta’azzara, da nufin kwace iko da birnin da kuma raba mazauna birnin da tilastawa kauracewa gidajensu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar ‘Yan Sahayoniyya Kan Gaza August 11, 2025 Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza August 11, 2025 Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Harin Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza August 11, 2025 Iran: Ba a yanke wani abu game da tattaunawa da Washington ba August 11, 2025 Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza August 11, 2025 Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari August 11, 2025 Chadi: An Daure Wani Dan Adawa Shekaru 20 A Gidan Kaso Da tara August 10, 2025 Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin August 10, 2025 Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasus Ko Rasha Bata taimaka ba August 10, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza
Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya gudanar da zaman gaggawa a hedikwatar MDD da ke birnin New York a jiya Lahadi, bayan matakin da majalisar ministocin Isra’ila ta dauka na fadada ayyukan soji da kuma mamaye yankin zirin Gaza.
Mataimakiyar Sakatare-Janar mai kula da harkokin Turai, Tsakiyar Asiya da Amurka, Miroslav Jenča, ta jaddada a yayin zaman cewa, “ba za a iya dakatar da dimbin wahalhalun jin kai da ake fama da su a Gaza ba, sai ta hanyar tsagaita bude wuta nan take kuma mai dorewa,” tana mai kira da a gaggauta sakin dukkan fursunoni ba tare da wani sharadi ba.
Jenča ta yi kira ga Isra’ila da ta bi abin da ya rataya a wuyanta a karkashin dokar jin kai ta kasa da kasa, ta ba da damar isar da kayan agaji cikin gaggawa kuma cikin aminci, ba tare da tsangwama ko kawo cikas ga wanann shiri ba, da kuma barin isar da kayan ga jama’a, tana mai jaddada bukatar “kare fararen hula, gami da ma’aikatan jin kai da masu neman taimako.”
A nasa bangaren, wakilin Aljeriya a MDD Ammar Benjamaa ya ce Isra’ila ba ta damu da dokokin kasa da kasa ko kuma bil’adama ba, ya kara da cewa “Isra’ilawa suna nuna rashin tausayi, Rashin Imani da dabi’a na dabbanci, suna kawar da Palasdinawa daga matsayinsu na yan Adam tare da kaskantar da su zuwa matsayin dabbobi kamar yadda suke gani.”
A martanin da ta mayar, wakiliyar Amurka ta dindindin a Majalisar Dinkin Duniya, Dorothy Shea, ta dora alhakin dukkanin abin da Isra’ila take aikatawa a kan Hamas.
Dangane da matakin da Isra’ila ta dauka na Shirin mamaye Gaza, ministocin harkokin wajen kasashen Australia, Jamus, Italiya, New Zealand, da Birtaniya sun sanar da kin amincewa da matakin na Isra’ila, tare da jaddada aniyarsu ta bai daya wajen aiwatar da yarjejeniyar kafa kasashe biyu ta hanyar yin shawarwari.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari August 11, 2025 Chadi: An Daure Wani Dan Adawa Shekaru 20 A Gidan Kaso Da tara August 10, 2025 Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin August 10, 2025 Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasus Ko Rasha Bata taimaka ba August 10, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya August 10, 2025 An Zabi Alkalan Wasa Biyu Daga Kasar Iran Don Alkalanci A gasar Kwallon Kafa ta Mata August 10, 2025 Kasar Iran Ta Yi Allah Wadai Da Bukatar ‘Yan Sahayoniyya Ta Son Kwace Zirin Gaza August 10, 2025 Iran Ta Cimma Matsayi A Yaki Kwanaki 12 August 10, 2025 Jami’an Tsaron Iran Sun Murkushe ‘Yan Ta’adda Kan Ofishin ‘Yan Sanda A Kudu Maso Gabashin Kasar August 10, 2025 Jefa Agajin Abinci Ta Sama A Zirin Gaza Ya Janyo Shahadan Falasdinawa 23 Tare Da Jikkata Wasu 124 August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci