Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince ta bada sama da naira miliyan 156 domin sayen tikitin jirgi na mayar da daliban jihar masu karatun likita har su 184 da suka kammala hutun su a gida zuwa makaranta a kasar Cyprus.

Shugaban Hukumar Bada Tallafin Karatu ta Jihar, Alhaji Saidu Magaji, ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse, Babban Birnin Jihar.

A cewar sa, tuni rukunin farko na dalibai mata su 31 suka tashi ta filin jirgin saman ikko zuwa Istanbul inda za’a dauke su zuwa kasar Cyprus don fara sabon zangon karatu.

Alhaji Sa’idu Magaji wanda yake tare da daliban kafin tashin su, ya yaba da kulawar Gwamna Umar Namadi kan tallafawa daliban jihar domin ci gaba da karatun su.

Kazalika, ya nuna jin dadi da irin kulawar kwamishinan Ilmi mai zurfi ga daliban Jigawa dake karatu a ciki da kuma wajen kasar nan.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewar, daliban jihar Jigawan su 184 masu karatun aikin likita a kasar Cyprus sun zo hutu bayan kammala zango na biyu na karatun su kamar yadda gwamnatin ta yi alkawarin kawo su hutu idan sun kammala zango na biyu na karatun su.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

 

A gaskiya wannan yanayi ya yi matukar burge ni, kuma sai na zaci ko don saboda ina bako ne, amma yayin da na ga wasu Sinawa suna daukar hotunan bishiyoyin, sai na ce to, babu makawa wannan yanayi ne mai burge kowa da kowa, bako da dan gari kuma ciki har da dattawa. Nan take ni ma na zaro wayata, muka ci gaba da kashe hotuna ni da abokin aikina. Na yi kokarin nuna kawaici a kan yadda yanayin ya shaukantar da ni, amma sai na ga abokin nawa ya fi ni “jazabancewa”, domin shi ya fi ni yawan yin “style” na daukar hoton da kuma yawan hotunan da muka dauka.

 

Wani abu da na lura da shi a kasar Sin shi ne, ba kawai a manyan birane ba, hatta a garuruwa na gundumomi, kasar ta samar da lambuna masu furanni da koramu da itatuwa masu ban sha’awa, inda iyalai suke zuwa domin shakatawa musamman da maraice bayan tasowa daga makaranta.

 

Ni dai, idan wani mai yawon shaktawa ya tambaye ni, wane lokaci ne mafi dacewa ya kawo ziyara kasar Sin, zan ce masa ka zo a lokacin “yanayi mai launin zinare”, watau a lokacin kaka, musamman daga karshen watan Oktoba kafin shiga yanayin hunturu sosai lokacin da wannan launi zai sauya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya November 5, 2025 Daga Birnin Sin An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou November 5, 2025 Daga Birnin Sin Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE  November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko
  • NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya
  • Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i
  • Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu
  • Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 
  • Likitoci sun wayar da kan mata kan cutar Sankara a Gombe